ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fintiri Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Fiye Da Naira Biliyan 486 Ga Majalisar Dokokin Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh and Sulaiman
1 year ago
Fintiri

Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya gabatar da kudirin kasafin kudin shekarar 2025 na Naira biliyan 486.218 a gaban majalisar dokokin jihar a ranar Litinin. 

 

A cewar Gwamnan, a lokacin da yake gabatar da kasafin mai taken “Budget of Service” ga majalisar dokokin jihar ya ce kasafin kudin da ake shirin yi ya nuna karin kashi dari bisa dari idan aka kwatanta da kasafin kudin shekarar 2024.

ADVERTISEMENT
  • Da Ɗumi-ɗumi: Majalisar Dokokin Jihar Adamawa Ta Amince Da Ƙudirin Ƙirƙiro Sabbin Gundumomi

Finitiri ya ce daga cikin kasafin kudi na naira biliyan 486 na kudaden da ake kashewa a kai a kai za su kai naira biliyan 137, wato kashi 28.23%, ragowar Naira biliyan 348, wato kashi 71.77%, za a kashesu ga manyan ayyuka.

 

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

Ya ce gwamnatinsa ta yi alkawarin cimma manufofinta guda takwas, wato tsaro, samar da ababen more rayuwa, kiwon lafiya, wadatar abinci, da ilimi a cikin wannan kasafin kudin 2025.

 

Gwamna Fintiri ya ce an kuma ware kasafin Naira biliyan 88 domin gina tituna a fadin jihar, ya bayyana kudirin gwamnatin na inganta hanyoyin sufurin kayayyaki a jihar.

 

“Muna sa ne da muhimmancin da ya wajaba a kanmu na hada garuruwa da hanyoyin mota domin saukaka wa da fadada tattalin arzikinmu cikin gaggawa,” in ji shi.

 

Majalisar karkashin jagorancin kakakin majalisar Rt. Hon Bathiya Wesley, tun daga lokacin ta karanto kudirin dokar a karo na 2 kuma ta mika kudurin kasafin ga kwamitin kudi, da kasafin kudi domin tantancewa.

 

Karatu na biyu ya biyo bayan kudirin da shugaban masu rinjaye Hon. Kate Raymond Mamuno (Mazabar Demsa) da Hon. Musa Mahmud Kallamu (Mayo Belwa).

 

Da yake jawabi a takaice gabatar da kasafin kudin, shugaban majalisar Rt. Hon Bathiya Wesley, ta yabawa gwamnan bisa nasarar gabatar da kasafin kudin shekarar 2025.

 

Haka kuma ya bada tabbacin shirye shiryen majalisar karkashin jagorancinsa na yin duk abin da ya dace domin ganin an gaggauta zartar da kasafin kudin da ake son aiwatarwa a shekarar 2025.

Fintiri
Muh'd Shafi'u Saleh
+ posts Bio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa
Fintiri
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  
  • Sulaiman
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • Sulaiman
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

MASU ALAKA

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya
Manyan Labarai

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tswaita Aiwatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Zuwa 30 Ga Watan Satumba

June 11, 2026
Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.
Manyan Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ƙudirin Dokar Kafa ‘Yansandan Jihohi.

June 11, 2026
Next Post
Kano

Gwamnan Kano Ya Naɗa Tsohon Shugaban Ma’aikatan Jihar Da Wasu 5 A Matsayin Kwamishinoni

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

Sin Ta Fitar Da “Shirin Aiki Na Kasa Kan Hakkin Dan Adam Na (2026-2030)”  

June 11, 2026
Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

Afirka Ta Kudu Ta Kafa Mummunan Tarihi A Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya

June 11, 2026
Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar

June 11, 2026
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Matsalar Tsaro: Manoma Sun Koma Gonakinsu A Katsina – Dikko Radda

June 11, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama

June 11, 2026
Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

June 11, 2026
An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

An Rufe Makarantu A Mexico Saboda Fara Gasar Kofin Duniya

June 11, 2026
An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

An Kaddamar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Dan Adam Na Shekarar 2026 A Beijing

June 11, 2026
Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

Kwararrun Sin Da Na DRC Sun Tattauna Matakan Hadin Gwiwa Na Dakile Cutar Ebola

June 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.