• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Jaddada Hadin Kai Da Hadin Gwiwa A Taron Davos

byCMG Hausa
2 years ago
新华社照片,天津,2023年6月27日
李强出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞
6月27日上午,国务院总理李强在天津出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞。
新华社记者 王晔 摄

新华社照片,天津,2023年6月27日 李强出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞 6月27日上午,国务院总理李强在天津出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞。 新华社记者 王晔 摄

A yau Talata ne, firaministan kasar Sin Li Qiang ya jaddada hadin kai da hadin gwiwa a lokacin da yake jawabi wajen bude taron shekara-shekara na sabbin zakaru karo na 14, wanda ake kira da Davos na bazara, a gundumar Tianjin dake arewacin kasar Sin.

  • Mataimakiyar Sakatare Janar Na MDD Na Ziyara A Kasar Sin 

Li ya ce, a cikin shekaru ukun da suka gabata, dukkan kasashe sun yi matukar fafatawa da cutar COVID-19, wacce ta nuna karfin hadin kan dan Adam tare da kula da juna a cikin mawuyacin hali.

Ya kara da cewa, babu wata kasa da za ta zauna lami-lafiya a yayin da ake fuskantar tashin hankali ba tare da ta nemi ɗauki daga sauran kasashe ba. Bugu da kari, bil’adama na fuskantar kalubale a duniya kamar sauyin yanayi, haɗarin bashi, da tafiyar hawainiyar bunkasuwa, da gibin arziki.

Li ya kuma ce, zalunci da wasu nau’in danniya, har ma da yake-yake na cikin gida, da rikice-rikicen yankuna a cikin ’yan shekarun nan, ba kawai sun jawo babbar bala’i ga jama’ar yankunan da abin ya shafa ba, har ma sun haddasa babbar illa ga ci gaban duniya.

Ya kuma bukaci a yi kokarin tabbatar da gaskiya da adalci, da yin aiki tukuru don magance matsalar tsaro, tare da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali don ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Sannan firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci taron tattaunawa na ’yan kasuwa, a yayin taron koli na tattauna tattalin arzikin duniya dake gudana a birnin Tianjin, inda ya yi musayar raayi da wakilan ’yan kasuwa.

Darakta janar ta hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO, Ngozi Okonjo Iweala da kimanin ’yan kasuwa 120 daga kasashe da yankuna sama da 20 ne suka halarci taron.

Bayan sauraron jawaban da wakilan ’yan kasuwa mahalartar taron suka gabatar, Li Qiang ya ce abun da aka fi bukata a duniya shi ne tuntubar juna da musaya, kuma abu mafi muhimmanci shi ne hadin gwiwa bisa adalci.

Ya ce ba kan ci gabanta kadai ta ke mayar da hankali ba, kasar Sin tana kuma gabatar da damarmakin samun ci gaba ga dukkan bangarori. A cewarsa, Sin kasa ce mai bude kofa, mai tafiya da kowa, kuma sahihiya.

Ya ce a shirye suke su hada hannu da ’yan kasuwa daga mabanbantan kasashe wajen ingiza karin kuzari ga habaka tattalin arzikin duniya. (Masu Fassarawa: Yahaya Babs, Faiza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version