• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Jaddada Hadin Kai Da Hadin Gwiwa A Taron Davos

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Firaministan Kasar Sin Ya Jaddada Hadin Kai Da Hadin Gwiwa A Taron Davos

新华社照片,天津,2023年6月27日 李强出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞 6月27日上午,国务院总理李强在天津出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞。 新华社记者 王晔 摄

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata ne, firaministan kasar Sin Li Qiang ya jaddada hadin kai da hadin gwiwa a lokacin da yake jawabi wajen bude taron shekara-shekara na sabbin zakaru karo na 14, wanda ake kira da Davos na bazara, a gundumar Tianjin dake arewacin kasar Sin.

  • Mataimakiyar Sakatare Janar Na MDD Na Ziyara A Kasar Sin 

Li ya ce, a cikin shekaru ukun da suka gabata, dukkan kasashe sun yi matukar fafatawa da cutar COVID-19, wacce ta nuna karfin hadin kan dan Adam tare da kula da juna a cikin mawuyacin hali.

Ya kara da cewa, babu wata kasa da za ta zauna lami-lafiya a yayin da ake fuskantar tashin hankali ba tare da ta nemi ɗauki daga sauran kasashe ba. Bugu da kari, bil’adama na fuskantar kalubale a duniya kamar sauyin yanayi, haɗarin bashi, da tafiyar hawainiyar bunkasuwa, da gibin arziki.

Li ya kuma ce, zalunci da wasu nau’in danniya, har ma da yake-yake na cikin gida, da rikice-rikicen yankuna a cikin ’yan shekarun nan, ba kawai sun jawo babbar bala’i ga jama’ar yankunan da abin ya shafa ba, har ma sun haddasa babbar illa ga ci gaban duniya.

Ya kuma bukaci a yi kokarin tabbatar da gaskiya da adalci, da yin aiki tukuru don magance matsalar tsaro, tare da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali don ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Sannan firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci taron tattaunawa na ’yan kasuwa, a yayin taron koli na tattauna tattalin arzikin duniya dake gudana a birnin Tianjin, inda ya yi musayar raayi da wakilan ’yan kasuwa.

Darakta janar ta hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO, Ngozi Okonjo Iweala da kimanin ’yan kasuwa 120 daga kasashe da yankuna sama da 20 ne suka halarci taron.

Bayan sauraron jawaban da wakilan ’yan kasuwa mahalartar taron suka gabatar, Li Qiang ya ce abun da aka fi bukata a duniya shi ne tuntubar juna da musaya, kuma abu mafi muhimmanci shi ne hadin gwiwa bisa adalci.

Ya ce ba kan ci gabanta kadai ta ke mayar da hankali ba, kasar Sin tana kuma gabatar da damarmakin samun ci gaba ga dukkan bangarori. A cewarsa, Sin kasa ce mai bude kofa, mai tafiya da kowa, kuma sahihiya.

Ya ce a shirye suke su hada hannu da ’yan kasuwa daga mabanbantan kasashe wajen ingiza karin kuzari ga habaka tattalin arzikin duniya. (Masu Fassarawa: Yahaya Babs, Faiza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Nada Mace Shugabar Masu Rinjayen Majalisar Dokokin Adamawa

Next Post

Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

Related

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

10 hours ago
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

11 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

12 hours ago
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

13 hours ago
An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO
Daga Birnin Sin

An Sanya Kaburburan Sarakunan Daular Xixia Ta Kasar Sin Cikin Muhimman Wuraren Tarihi Na UNESCO

15 hours ago
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

1 day ago
Next Post
Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.