ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Jaddada Hadin Kai Da Hadin Gwiwa A Taron Davos

by CMG Hausa
3 years ago
新华社照片,天津,2023年6月27日
    李强出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞
    6月27日上午,国务院总理李强在天津出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞。
    新华社记者 王晔 摄

新华社照片,天津,2023年6月27日 李强出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞 6月27日上午,国务院总理李强在天津出席2023年夏季达沃斯论坛开幕式并致辞。 新华社记者 王晔 摄

A yau Talata ne, firaministan kasar Sin Li Qiang ya jaddada hadin kai da hadin gwiwa a lokacin da yake jawabi wajen bude taron shekara-shekara na sabbin zakaru karo na 14, wanda ake kira da Davos na bazara, a gundumar Tianjin dake arewacin kasar Sin.

  • Mataimakiyar Sakatare Janar Na MDD Na Ziyara A Kasar Sin 

Li ya ce, a cikin shekaru ukun da suka gabata, dukkan kasashe sun yi matukar fafatawa da cutar COVID-19, wacce ta nuna karfin hadin kan dan Adam tare da kula da juna a cikin mawuyacin hali.

Ya kara da cewa, babu wata kasa da za ta zauna lami-lafiya a yayin da ake fuskantar tashin hankali ba tare da ta nemi ɗauki daga sauran kasashe ba. Bugu da kari, bil’adama na fuskantar kalubale a duniya kamar sauyin yanayi, haɗarin bashi, da tafiyar hawainiyar bunkasuwa, da gibin arziki.

ADVERTISEMENT

Li ya kuma ce, zalunci da wasu nau’in danniya, har ma da yake-yake na cikin gida, da rikice-rikicen yankuna a cikin ’yan shekarun nan, ba kawai sun jawo babbar bala’i ga jama’ar yankunan da abin ya shafa ba, har ma sun haddasa babbar illa ga ci gaban duniya.

Ya kuma bukaci a yi kokarin tabbatar da gaskiya da adalci, da yin aiki tukuru don magance matsalar tsaro, tare da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali don ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sannan firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci taron tattaunawa na ’yan kasuwa, a yayin taron koli na tattauna tattalin arzikin duniya dake gudana a birnin Tianjin, inda ya yi musayar raayi da wakilan ’yan kasuwa.

Darakta janar ta hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO, Ngozi Okonjo Iweala da kimanin ’yan kasuwa 120 daga kasashe da yankuna sama da 20 ne suka halarci taron.

Bayan sauraron jawaban da wakilan ’yan kasuwa mahalartar taron suka gabatar, Li Qiang ya ce abun da aka fi bukata a duniya shi ne tuntubar juna da musaya, kuma abu mafi muhimmanci shi ne hadin gwiwa bisa adalci.

Ya ce ba kan ci gabanta kadai ta ke mayar da hankali ba, kasar Sin tana kuma gabatar da damarmakin samun ci gaba ga dukkan bangarori. A cewarsa, Sin kasa ce mai bude kofa, mai tafiya da kowa, kuma sahihiya.

Ya ce a shirye suke su hada hannu da ’yan kasuwa daga mabanbantan kasashe wajen ingiza karin kuzari ga habaka tattalin arzikin duniya. (Masu Fassarawa: Yahaya Babs, Faiza Mustapha)

Davos
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

Jarumar Nollywood, Mercy Ta Sauke Farali A Saudiyya Bayan Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.