• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Ziyarci Yankunan Da Suka Yi Fama Da Bala’in Girgizar Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ziyarci yankunan da suka sha fama da girgizar kasa a arewa maso yammacin kasar Sin a jiya Asabar, inda ya yi kira da a dauki dukkanin matakan da suka kamata, wajen kyautata yanayin rayuwar mazauna wuraren.

Li, ya ziyarci kauyuka da dama a gundumar Jishishan dake lardin Gansu, da gundumar Minhe dake lardin Qinghai mai makwaftaka.

  • Tsohon Firaministan Belgium: Ya Dace EU Ta Nuna Matsayar Kanta A Maimakon Kasancewa ‘Yar Koren Amurka
  • MDD Ta Sanar Da Bikin Bazara Na Sin A Matsayin Daya Daga Bukukuwan Da Za A Rika Kiyaye Kimarsu

Yayin ziyarar ta sa ya zanta kai tsaye da mutanen da ibtila’in ya shafa, ya kuma ji yadda ayyukan samar musu matsugunai, da tallafin jin kai, da sake gina wuraren zaman su ke gudana. Kaza lika, ya ce muhimmin abun da ake so a cimma nasarar sa cikin ayyukan jin kai shi ne tabbatar da jama’ar da bala’in ya shafa sun samu muhalli mai kyau mai dumi a wannan lokaci na hunturu.

Firaministan na Sin ya kara jaddada kira ga ma’aikatan jin kai da su kara azamar samar da kayayyakin bukata, da na amfanin yau da kullum ga mazauna wadannan yankuna, tare da gina gidajen wucin gadi cikin sauri ga wadanda ke zaune a tantuna.

Ya kuma ba da umarnin sake duba gine gine, da karfafa wadanda suka kamata, ta yadda mutane za su iya komawa, tare da samun damar sake bude muhimman ababen more rayuwa kamar makarantu da asibitoci.

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Da misalin karfe 12 saura minti 1 na daren ranar Litinin din makon jiya ne girgizar kasar mai karfin maki 6.2 ta auku. Kuma ya zuwa ranar Juma’a, adadin wadanda ta hallaka ya kai mutane 148, baya ga mutane 781 da suka jikkata. Kana ibtila’in ya lalata gine gine da dama. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

Yaduwar Juyin Mulki A Afirka

November 7, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.