• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Ziyarci Yankunan Da Suka Yi Fama Da Bala’in Girgizar Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ziyarci yankunan da suka sha fama da girgizar kasa a arewa maso yammacin kasar Sin a jiya Asabar, inda ya yi kira da a dauki dukkanin matakan da suka kamata, wajen kyautata yanayin rayuwar mazauna wuraren.

Li, ya ziyarci kauyuka da dama a gundumar Jishishan dake lardin Gansu, da gundumar Minhe dake lardin Qinghai mai makwaftaka.

  • Tsohon Firaministan Belgium: Ya Dace EU Ta Nuna Matsayar Kanta A Maimakon Kasancewa ‘Yar Koren Amurka
  • MDD Ta Sanar Da Bikin Bazara Na Sin A Matsayin Daya Daga Bukukuwan Da Za A Rika Kiyaye Kimarsu

Yayin ziyarar ta sa ya zanta kai tsaye da mutanen da ibtila’in ya shafa, ya kuma ji yadda ayyukan samar musu matsugunai, da tallafin jin kai, da sake gina wuraren zaman su ke gudana. Kaza lika, ya ce muhimmin abun da ake so a cimma nasarar sa cikin ayyukan jin kai shi ne tabbatar da jama’ar da bala’in ya shafa sun samu muhalli mai kyau mai dumi a wannan lokaci na hunturu.

Firaministan na Sin ya kara jaddada kira ga ma’aikatan jin kai da su kara azamar samar da kayayyakin bukata, da na amfanin yau da kullum ga mazauna wadannan yankuna, tare da gina gidajen wucin gadi cikin sauri ga wadanda ke zaune a tantuna.

Ya kuma ba da umarnin sake duba gine gine, da karfafa wadanda suka kamata, ta yadda mutane za su iya komawa, tare da samun damar sake bude muhimman ababen more rayuwa kamar makarantu da asibitoci.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Da misalin karfe 12 saura minti 1 na daren ranar Litinin din makon jiya ne girgizar kasar mai karfin maki 6.2 ta auku. Kuma ya zuwa ranar Juma’a, adadin wadanda ta hallaka ya kai mutane 148, baya ga mutane 781 da suka jikkata. Kana ibtila’in ya lalata gine gine da dama. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.