• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Singapore

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Firaministan Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Singapore
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya ne, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya tattauna da takwaransa na kasar Singapore Lee Hsien Loong da ke ziyara a nan birnin Beijing,fadar mulkin kasar Sin inda sassa biyu suka sha alwashin ci gaba da yin hadin gwiwa.

Li ya bayyana cewa, a matsayin Lee na tsohon abokin da Sinawa suka saba da shi, kuma daya daga cikin rukunin farko na shugabannin ketare da ya tarba, tun bayan da ya zama firaministan majalisar gudanarwar kasar Sin, wannan ya nuna cewa, kasashen Sin da Singapore, sun dora muhimmanci matuka kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore

Ya ce, yayin da kasashen Sin da Singapore ke tsayawa tsayin daka, wajen kare dunkulewar tattalin arziki da zamantakewar al’ummar duniya daban-daban, a hannu guda kasarsa tana son hada kai da bangaren Singapore, don yin hadin gwiwa don nuna adawa da yunkurin siyasantar da batutuwan tattalin arziki, da wuce gona da iri kan batun tsaron kasa, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, da tsarin tafiyar da harkokin masana’antu da samar da kayayyaki, da tabbatar da tsarin ciniki tsakanin sassa daban-daban, bisa jagorancin kungiyar cinikayya ta duniya.

A nasa bangare Lee Hsien Loong ya lura da cewa, kasar Sin a matsayinta na daya daga cikin manyan abokan hadin gwiwar ASEAN, dukkan kasashen Asiya suna goyon bayan raya hulda da kasar Sin, kuma suna fatan karfafa hadin gwiwa tare da yin amfani da damar da kasar Sin ta samu, wajen farfado da tattalin arzikinta da kara bude kofarta ga kasashen waje bayan annobar COVID-19.

Ya kara da cewa, kasar Singapore tana maraba tare da goyon bayan kokarin kasar Sin, na shiga yarjejeniyar hadin gwiwar tattalin arziki na zamani da cikakkiyar yarjejeniyar abokantaka a tsakanin kasashen dake yankin tekun Pacific, kuma tana son hada kai tare da kasar Sin wajen tabbatar da tsarin ciniki na kasa da kasa bisa gaskiya, mai salon bude kofa. (Ibrahim)

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Saudiyya Ta Damke Bakin Haure Sama Da 16,000

Next Post

Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

1 day ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.