ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Singapore

by CMG Hausa
3 years ago
Singapore

A jiya ne, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya tattauna da takwaransa na kasar Singapore Lee Hsien Loong da ke ziyara a nan birnin Beijing,fadar mulkin kasar Sin inda sassa biyu suka sha alwashin ci gaba da yin hadin gwiwa.

Li ya bayyana cewa, a matsayin Lee na tsohon abokin da Sinawa suka saba da shi, kuma daya daga cikin rukunin farko na shugabannin ketare da ya tarba, tun bayan da ya zama firaministan majalisar gudanarwar kasar Sin, wannan ya nuna cewa, kasashen Sin da Singapore, sun dora muhimmanci matuka kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Firaministan Spaniya Da Na Malaysia Da Na Singapore

Ya ce, yayin da kasashen Sin da Singapore ke tsayawa tsayin daka, wajen kare dunkulewar tattalin arziki da zamantakewar al’ummar duniya daban-daban, a hannu guda kasarsa tana son hada kai da bangaren Singapore, don yin hadin gwiwa don nuna adawa da yunkurin siyasantar da batutuwan tattalin arziki, da wuce gona da iri kan batun tsaron kasa, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, da tsarin tafiyar da harkokin masana’antu da samar da kayayyaki, da tabbatar da tsarin ciniki tsakanin sassa daban-daban, bisa jagorancin kungiyar cinikayya ta duniya.

ADVERTISEMENT

A nasa bangare Lee Hsien Loong ya lura da cewa, kasar Sin a matsayinta na daya daga cikin manyan abokan hadin gwiwar ASEAN, dukkan kasashen Asiya suna goyon bayan raya hulda da kasar Sin, kuma suna fatan karfafa hadin gwiwa tare da yin amfani da damar da kasar Sin ta samu, wajen farfado da tattalin arzikinta da kara bude kofarta ga kasashen waje bayan annobar COVID-19.

Ya kara da cewa, kasar Singapore tana maraba tare da goyon bayan kokarin kasar Sin, na shiga yarjejeniyar hadin gwiwar tattalin arziki na zamani da cikakkiyar yarjejeniyar abokantaka a tsakanin kasashen dake yankin tekun Pacific, kuma tana son hada kai tare da kasar Sin wajen tabbatar da tsarin ciniki na kasa da kasa bisa gaskiya, mai salon bude kofa. (Ibrahim)

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya
Daga Birnin Sin

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
Daga Birnin Sin

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Next Post
Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

Firaministan Kwadibuwa Na Sa Ran Za A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

Yadda Ake Miyar Margi (Margi Special)

November 15, 2025
Yadda Za Ku Gyara Kanku

Yadda Za Ku Gyara Kanku

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.