ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Sin Ya Yi Kira Ga Membobin G20 Da Su Goyi Bayan Salon Cinikayya Cikin ’Yanci

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
G20

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya yi kira ga kasashe membobin kungiyar G20 da su rungumi juna, su ingiza tsarin cinikayya cikin ‘yanci, da gina budadden salon raya tattalin arzikin duniya, a gabar da farfadowar tattalin arzikin duniya ke tafiyar hawainiya.

Li, ya bayyana hakan ne cikin jawabinsa a zama na farko na taron G20 karo na 20, dake gudana a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu. Zaman dai ya mayar da hankali ne ga dunkule dukkanin sassa, da wanzar da ci gaban tattalin arziki, ya kuma gudana karkashin jagorancin shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa.

Firaministan na Sin ya ce tattalin arzikin duniya ya sake gamuwa da manyan kalubale, ciki har da farfadowar daukar matakai daga bangare guda, da kariyar cinikayya, da ma karuwar shingayen cinikayya da fito-na-fito. Daga nan sai ya yi kira ga kungiyar ta G20 da ta tunkari wadannan matsaloli yadda ya kamata, ta lalubo matakan magancesu, da taimakawa wajen hado kan dukkanin sassa masu ruwa da tsaki, zuwa turbar goyon bayan juna da hadin gwiwa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ya yi kira da a kara azamar daga muryoyin kasashe masu tasowa, da gina tsarin adalci, da budaddiyar odar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen duniya.

A cewarsa, kasar Sin ta fitar da tsarin gudanar da matakai, wadanda za su tabbatar da an aiwatar da manufofin G20 na bunkasa masana’antu a nahiyar Afirka da sauran kasashe masu karancin ci gaba. Yana mai jaddada aniyar Sin ta ingiza salon samar da ci gaban bai daya na dukkanin kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Bugu da kari, Li ya ce Sin na goyon bayan rage basukan da ake bin kasashe masu tasowa, ta kuma shiga wani shiri tare da Afirka ta kudu, na tallafawa bunkasa masana’antu a Afirka. Kuma Sin din za ta kafa cibiyar kasa da kasa ta samar da ci gaba. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Yi Kira Ga Japan Da Ta Zurfafa Tunani Tare Da Gaggauta Gyara Kura-kuranta

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Yi Kira Ga Japan Da Ta Zurfafa Tunani Tare Da Gaggauta Gyara Kura-kuranta

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.