• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fyade: An Yanke Wa Robinho Zaman Gidan Kaso Na Shekara Tara

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Fyade: An Yanke Wa Robinho Zaman Gidan Kaso Na Shekara Tara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotu a kasar Brazil ta sanar da cewa tsohon dan kwallon Manchester City da Real Madrid, Robinho, zai yi zaman gidan kaso na tsawon shekara tara sakamakon hukuncin laifin yin fyade.

An samu Robinho mai shekara 40 da laifi a wata kotu a Italiya a shekara ta 2017, wanda yana cikin taron dangin fyaden da aka yi wa wata mata ‘yar Albania ‘yar shekara 22.

  • Kamfanonin Hakar Ma’adanai 40 Sun Samu Lasisi A Jihar Edo
  • Rundunar ‘Yansandan Bauchi Ta Fara Cafko Masu Garkuwa Ta Amfani Da Fasahar Zamani

Dan kwallon yana zaune a Brazil, wanda ba a mika shi Italiya ba, to amma alkalai a Brazil sun yanke hukunci ranar Laraba cewar zai yi zaman yari a kasar kamar yadda Italiya ta bukata.

Lauyoyi sun ce yana da lokacin da zai daukaka kara kafin hukuncin ya fara aiki a kansa amma idan har lokaci ya wuce ko kuma ya yanke shawarar ba zai daukaka kara ba to hukuncin zai fara aiki.

Tsohon dan wasan tawagar Brazil din da ya buga wa kasar wasa 100, yana buga wasa a kungiyar kwal-lon kafa ta AC Milan ne a lokacin da aka aikata laifin da aka zarge shi da yi.

Labarai Masu Nasaba

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

A shekarar 2020 aka samu dan wasan da laifin aikata fyaden, bayan da ya yi rashin nasarar daukaka kara, inda wata kotu a Italiya ta tabbatar masa da hukuncin, sai dai daga nan ne masu shigar da kara a Italiya suka mika takardun izinin kamo shi daga Brazil. Robinho wanda ya yi kakar wasa biyu a Manchester City, ya sanar da wani kamfanin dillacin labarai a Brazil cewar da amincewar matar aka yi lalata da ita ba fyade aka yi mata ba.

Dan wasan ya dauki kofin La Liga biyu a kaka hudun da ya yi a Real Madrid daga nan ya koma kungiyar Manchester City a matakin wanda aka saya mafi tsada a Burtaniya kan kudi fam miliyan 32.5.

An kuma sayi dan kwallon a ranar karshe da za a rufe kasuwar cinikin ‘yan kwallo a Satumbar shekara ta 2008 – kuma a karon farko da Sheikh Mansour ya fara aiki a matakin wanda ya mallaki Manchester City.

Bayan kakar wasa biyu da Manchester City daga nan ya koma AC Milan, kungiyar da ya yi kaka biyar daga nan ya koma kasar China a kungiyar kwallon kafa ta Guangzhou Ebergrande inda bayan da ya bar China ne sai ya koma kungiyar Atletico Mineiro a Brazil.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dambarwar Amal Umar Da ‘Yansanda, Ina Aka Kwana?

Next Post

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (5)

Related

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

3 days ago
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Wasanni

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

3 days ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

3 days ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

4 days ago
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
Wasanni

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

4 days ago
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool
Wasanni

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool

5 days ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (5)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (5)

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.