• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ga Dukkan Alamu Japan Ta Zama Butulu

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Japan

FILE - The Fukushima Daiichi nuclear power plant, damaged by a massive March 11, 2011, earthquake and tsunami, is seen from the nearby Ukedo fishing port in Namie town, northeastern Japan, Thursday, Aug. 24, 2023. For the wrecked Fukushima Daiichi nuclear plant, managing the ever-growing radioactive water held in more than 1,000 tanks has been a safety risk and a burden since the meltdown in March 2011. The start of treated wastewater release Thursday marked a milestone for the decommissioning, which is expected to take decades. (AP Photo/Eugene Hoshiko, File)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zubar da ruwan dagwalon nulikiyar Japan a cikin teku na ci gaba da ɗaukar hankali a duniya yayin da shugabannin ƙasashe makwabta tekun Pacifik suka ci gaba da nuna adawarsu a bayyane a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 78.

Firaministan Tsibirin Solomon Manasseh Sogavare, a yayin da yake gabatar da jawabinsa a babban zauren muhawarar majalisar, ya caccaki ƙasar Japan, da rahoton tantancewa na Hukumar Makamashin Nukiliya (IAEA) ta Duniya game da rashin nuna gaskiya da cin zarafin ƙasashe mazauna yankin Pasifik.

  • “Mafarkina Na Zuwa Sararin Samaniya” 
  • Jarin Da Sinawa ‘Yan Kasuwa Masu Zaman Kansu Ke Zubawa A Angola Na Bunkasa Rayuwar ‘Yan Kasar

Bari mu dan waiwayi baya kaɗan, tarihi ya nuna cewa, shekaru goma sha biyu da suka gabata, bayan haɗarin nukiliyar Fukushima, Japan ta samu taimako daga sassa daban-daban a faɗin duniya. Bayan wadannan shekarun 12, Japan ta yanke shawarar sanya dukkan bil’adama cikin haɗarin gurɓacewar nukiliyarta. Alhalin Yarjejeniya ta shekarar 1972 kan rigakafin gurɓacewar ruwa ta hanyar zubar da sharar gida da sauran al’amura ta hana gurɓata teku, da kuma yarjejeniyar Majalisar Ɗinkin Duniya kan dokar teku ta tanadi cewa ƙasashe na da alhakin kare da kiyaye muhallin ruwa.

Gwamnatin Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya sama da tan miliyan guda a cikin teku. Mutane da dama sun fusata da wannan yunƙuri, ciki har da gwamnatoci da dama, waɗanda a hankali suna ganin wannan zaɓi a matsayin cin amanar al’umma da wulakanta amincin duniya.

Baya ga yin watsi da bayanan kimiyya, shawarar ta kuma keta dokar ruwa ta ƙasa da ƙasa da kuma ‘yancin ɗan Adam na mutanen Japan da Pacifik, musamman ma damuwar masunta.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Duk da damuwar al’ummar cikin gida da na ƙasa da ƙasa, Japan ta dage kan yin amfani da tekun Pasifik a matsayin “wurin zuba shararta” ta hanyar zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin tekun.

A daidai wannan gaɓar sai mu gabatar da wasu tambayoyi masu muhimmanci. Shin na’urorin tsarkake ko tsaftace tekun na Japan zasu ci gaba da yin aiki da kyau cikin shekaru talatin masu zuwa? A lokacin da ruwan dagwalon da ta zuba cikin tekun ta wuce iyakar mizani? Shin za a iya sanar da al’ummar duniya cikin gaggawa? Menene illar da wannan gubar zata yi wa teku na dogon lokaci akan tsaro da abinci, da lafiyar ɗan Adam, da yanayin ruwa? Rahoton Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) bai bayar da amsar wadannan tambayoyi ba.

Bugu da ƙari, gwamnatin ƙasar Japan na da niyyar sake kunna wutar lantarki da ƙarin makamashin nukiliya duk da alamun girgizar ƙasa da hatsarin tsaro, da bala’in nukiliyar da ke gudana, da kuma ɗimbin kuɗaɗen jama’a da ake buƙata. Bayan sanin cewa halin gaggawar da yanayin duniya ke ciki na buƙatar amintattun hanyoyin samar da makamashi mai tsafta, kamar iska da hasken rana, wadanda dabarun makamashi na gwamnatin ƙasar na yanzu ba za su iya samarwa ba.

A matsayin muhimmiyar hanyar kasuwancin duniya, Tekun Pasifik gida ne ga dukkan ƙasashen yankin. Dan Adam na iya fama da gurɓacewar tekun Pasifik, tare da sakamako mai illa. Kafin Japan ta yi wannan mummunar yunƙurin, an yi fatan hukumar ta IAEA za ta ɗauki ƙarin lokaci tare da zurfafa bincike, da yin la’akari da dukkan abubuwan da za su iya haifar da haɗari.

Dole ne dukkan gwamnatoci da ƙasashe da ke da alhakin sake tantance tasirin wannan mummunar shawarar ga bil’adama su farga. Kira anan ita ce a gudanar da bincike na biyu a cikin hanyar da ta dace kuma a kai ga yanke shawara mafi aminci ga bil’adama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJapanXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gyaran Amarya Kafin Lokacin Aure

Next Post

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattauna Dauwamammen Ci Gaban Aikin Sufuri

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Xi

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattauna Dauwamammen Ci Gaban Aikin Sufuri

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.