ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ga Dukkan Alamu Japan Ta Zama Butulu

by CGTN Hausa
3 years ago
Japan

FILE - The Fukushima Daiichi nuclear power plant, damaged by a massive March 11, 2011, earthquake and tsunami, is seen from the nearby Ukedo fishing port in Namie town, northeastern Japan, Thursday, Aug. 24, 2023. For the wrecked Fukushima Daiichi nuclear plant, managing the ever-growing radioactive water held in more than 1,000 tanks has been a safety risk and a burden since the meltdown in March 2011. The start of treated wastewater release Thursday marked a milestone for the decommissioning, which is expected to take decades. (AP Photo/Eugene Hoshiko, File)

Zubar da ruwan dagwalon nulikiyar Japan a cikin teku na ci gaba da ɗaukar hankali a duniya yayin da shugabannin ƙasashe makwabta tekun Pacifik suka ci gaba da nuna adawarsu a bayyane a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 78.

Firaministan Tsibirin Solomon Manasseh Sogavare, a yayin da yake gabatar da jawabinsa a babban zauren muhawarar majalisar, ya caccaki ƙasar Japan, da rahoton tantancewa na Hukumar Makamashin Nukiliya (IAEA) ta Duniya game da rashin nuna gaskiya da cin zarafin ƙasashe mazauna yankin Pasifik.

  • “Mafarkina Na Zuwa Sararin Samaniya” 
  • Jarin Da Sinawa ‘Yan Kasuwa Masu Zaman Kansu Ke Zubawa A Angola Na Bunkasa Rayuwar ‘Yan Kasar

Bari mu dan waiwayi baya kaɗan, tarihi ya nuna cewa, shekaru goma sha biyu da suka gabata, bayan haɗarin nukiliyar Fukushima, Japan ta samu taimako daga sassa daban-daban a faɗin duniya. Bayan wadannan shekarun 12, Japan ta yanke shawarar sanya dukkan bil’adama cikin haɗarin gurɓacewar nukiliyarta. Alhalin Yarjejeniya ta shekarar 1972 kan rigakafin gurɓacewar ruwa ta hanyar zubar da sharar gida da sauran al’amura ta hana gurɓata teku, da kuma yarjejeniyar Majalisar Ɗinkin Duniya kan dokar teku ta tanadi cewa ƙasashe na da alhakin kare da kiyaye muhallin ruwa.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya sama da tan miliyan guda a cikin teku. Mutane da dama sun fusata da wannan yunƙuri, ciki har da gwamnatoci da dama, waɗanda a hankali suna ganin wannan zaɓi a matsayin cin amanar al’umma da wulakanta amincin duniya.

Baya ga yin watsi da bayanan kimiyya, shawarar ta kuma keta dokar ruwa ta ƙasa da ƙasa da kuma ‘yancin ɗan Adam na mutanen Japan da Pacifik, musamman ma damuwar masunta.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Duk da damuwar al’ummar cikin gida da na ƙasa da ƙasa, Japan ta dage kan yin amfani da tekun Pasifik a matsayin “wurin zuba shararta” ta hanyar zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin tekun.

A daidai wannan gaɓar sai mu gabatar da wasu tambayoyi masu muhimmanci. Shin na’urorin tsarkake ko tsaftace tekun na Japan zasu ci gaba da yin aiki da kyau cikin shekaru talatin masu zuwa? A lokacin da ruwan dagwalon da ta zuba cikin tekun ta wuce iyakar mizani? Shin za a iya sanar da al’ummar duniya cikin gaggawa? Menene illar da wannan gubar zata yi wa teku na dogon lokaci akan tsaro da abinci, da lafiyar ɗan Adam, da yanayin ruwa? Rahoton Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) bai bayar da amsar wadannan tambayoyi ba.

Bugu da ƙari, gwamnatin ƙasar Japan na da niyyar sake kunna wutar lantarki da ƙarin makamashin nukiliya duk da alamun girgizar ƙasa da hatsarin tsaro, da bala’in nukiliyar da ke gudana, da kuma ɗimbin kuɗaɗen jama’a da ake buƙata. Bayan sanin cewa halin gaggawar da yanayin duniya ke ciki na buƙatar amintattun hanyoyin samar da makamashi mai tsafta, kamar iska da hasken rana, wadanda dabarun makamashi na gwamnatin ƙasar na yanzu ba za su iya samarwa ba.

A matsayin muhimmiyar hanyar kasuwancin duniya, Tekun Pasifik gida ne ga dukkan ƙasashen yankin. Dan Adam na iya fama da gurɓacewar tekun Pasifik, tare da sakamako mai illa. Kafin Japan ta yi wannan mummunar yunƙurin, an yi fatan hukumar ta IAEA za ta ɗauki ƙarin lokaci tare da zurfafa bincike, da yin la’akari da dukkan abubuwan da za su iya haifar da haɗari.

Dole ne dukkan gwamnatoci da ƙasashe da ke da alhakin sake tantance tasirin wannan mummunar shawarar ga bil’adama su farga. Kira anan ita ce a gudanar da bincike na biyu a cikin hanyar da ta dace kuma a kai ga yanke shawara mafi aminci ga bil’adama.

Japan
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Xi

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Tattauna Dauwamammen Ci Gaban Aikin Sufuri

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.