• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Game Da Tambayar Nan:  Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun ranar 7 ga watan Oktoba, tambayoyi da dama suke bijirowa a tsanake daga kafofin yada labaran Turawan Yamma iri daban-daban tare da yin amfani da su a matsayin gabatar da tattaunawa a gidajen talabijin dinsu da zimmar cewa, suna wakiltar masu kallo da sauraro. A wannan rubutu, zan kalubalanci daya daga cikin wadannan tambayoyi.

Bayan labari mai tsawo na abin da ya faru a safiyar ranar 7 ga watan Oktoba, ko shakka babu; labaran da aka kirkira aka kuma zuzuta su marasa dadi a kan Isra’ila, su ake ta sake maimaitawa, abin tambaya a nan shi ne, ko ka yi tir da wannan?
Babu shakka, dukkannin mu mun kalla a talabijin yadda mayakan Falastinawa suka mamaye iyakoki a 1967, sannan mun kwana da sanin yadda sojojin Isra’ila da dama suka mutu a wannan safiyar, haka nan yadda aka tasa keyar da dama daga cikin fararen hula na al’ummar Isra’ilan zuwa Gaza a matsayin fursunoni.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna
  • Sin: Ya Kamata Kwamitin Sulhu Ya Kara Daukar Matakai Kan Lokaci Don Inganta Tsagaita Bude Wuta Da Kawo Karshen Yaki A Dukkan Fannoni

Wannan bai kamata ya zama maudu’in da za a tattauna a kansa ba, in dai ba zancen kurame ake so mu yi ba. Don haka, da zarar an ga sun fara yin wannan tambayar tare da gabatarwa mai tsawo, to sun gama da kai, domin kuwa za a dauki hakan a matsayin wata babbar hujja. Sannan, za su nemi amsa ta kasance cikin dayan biyu, ko eh ko a’a. Wannan kai tsaye rashin adalci ne, dalili kuwa cewa eh ko a’a, yana nufin ka ware wannan rana kenan daga cikin kundin tarihin abin da ya faru.

A siyasa, musamman idan aka yi la’akari da abubuwan da suka faru tare da bayyana gaskiyar al’amarin abin day a wakana, muna bukatar isasshen fili domin tattauna wannan al’amari, idan kuma ba haka ba, za ta kai ga an tilasta mana daukan bangaranci, tun da ba mu da wani zabi. Idan kuma muka amince da cewa, wadannan yake-yake da wannan bala’i za a kawo karshensa ta bangarensu da kuma bangaren abin day a faru daga tarihi, ko shakka babu wannan zai bude hanyar kisan kare dangi.

Abin da ya faru a ranar 7 ga Oktoba ya riga ya faru, a cikin abubuwan da muke gani a shafukan sada zumunta da kididdigar da ake fitowa da ita, lallai akwai bukatar fito da abubuwa da dama da suke a boye tare da bayyana su kowa ya sani, daga nan gaskiyar za ta bayyana kuru-kuru. Sanin kowa ne, ba a bari al’umma su san sirrin da ke tattare da sojoji, tun da suna da salo da hanyoyin dabaru iri daban-daban wanda bas a so al’umma su sani.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

Ranar 7 ga watan Oktoba na da matukar tushe a tarihi, shekara 106 da ta gabata, Kasar Birtaniya ta shuka mummunan iri na rashin gaskiya, cin zarafi da kuma zalinci ga al’ummar Falastin, wanda ya yi sanadiyyar wahalar da suke fama da ita har zuwa yanzu ta hanyar fitar da mummunan sanarwar Balfour a ranar 2 ga watan Nuwambar 1917, wanda a wancan lokacin; Kasar Birtaniyar ba ta san komai na tarihi game da Falastin din ba.
A sanarwar da Birtaniyar ta bayar, ta mallaka wa Yahudawan Turai su gina kasar a matsayi kasa, ba tare da yin la’akari da asalin masu kasar ba da kuma hakkin da suke da shi dokance.

Ba za mu taba raba ranar 7 ga watan Oktoba daga Al-Nakba(ranar bala’i) ba tare da irin hukuncin da muka fuskanta a shekara 1948, bayan shekara 10 cif da ‘yan ta’addan Yahudawa da suka hada da Lehi, Irgun, da kuma Haganah suka yi wa ‘yan’uwanmu kisan kiyashi.

Abin day a faru a Deir Yasin da Hotel din King Dabid da kuma Al Tantura da sauran makamantansu, ba za mu taba mantawa da shi ba har abada, wanda wannan kisan kiyashin da aka yi wa Falastinawa ne ya yi sanadiyyar mafi yawancinsu zama ‘yan gudun hijira a Kasashen Lebanon, Siriya, Jodan, West Bank da kuma Gaza.

A shekarar 1948, bakin haure sun samu cikakken daurin gindi tare da gudunmawa daga wurin Turawan Kasashen Yamma, na korar Falastinawa tare da gina kasar da kashi 78 cikin 100 na tarihinta tamu ce.

Ba za taba tunawa da ranar 7 ga watan Oktoba ba tare da tunawa da ranar 6 ga watan Yunin 1967 ba, yayin da Isra’ila ta samu nasarar sake mamaye kasha 22 cikin 100 na Kasar Falastin mai cike da tarihi. Tun wancan lokaci, kimanin shekara 56 kenan suna fama da wannan zalinci da rashin adalci da fifikon Yahudawa a kan Falastinawa.
Ranar 7 ga watan Oktoba, ta fallasa Kasashen Yammacin Turai da dama ta fuskar son zuciyar shugabaninsu da amfani da kafafen yada labaransu, babu kunya babu tsoron Allah suna goyon bayan kai hari na ta’addanci a kan mutanen da suke da hakki a kan kayansu, wanda wannan zalinci ne karara.

Saboda haka, idan muka yi nasarar magance wannan matsala tun daga tushe tare da daga‘yan yatsunmu a kan damuwar da muke ci gaba da ji, ranar 7 ga watan Oktoba za ta kasance ranar da dukkannin mu za mu farka daga dogon baccin da muka jima muna yi, ma’ana, muna share fagen zaman lafiya mai dorewa kenan.

Har ila yau, amsar tambayar Falastinawa ta dogara ne ga dokokin kasa da kasa, kudirin majalisar dinkin duniya 181, 194, 242,388 da kuma wasu da dama daga cikin kudirorin majalisar dinkin duniyar wadanda za su sanya Falastin kasancewa cikin tsarin kasa mai zaman kanta tare da yi wa Falastinawan adalci wajen dawo da ‘yan gudun hijira kamar yadda kudirin majalisar dinkin duniya na 194 ya tanadar, ita ce kawai hanyar da ta dace wajen tabbatar da cewa, babu wata ranar 7 ga Oktoba da za a sake yi maimaita kisan kiyashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HamasIsra'ilaZirin gaza
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Next Post

Tashin Bom A Kaduna: Yadda Na Tsallake Rijiya Da Baya – Dattijo Mai Shekara 74

Related

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

1 hour ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Labarai

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

6 hours ago
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Labarai

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

7 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

8 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Tashin Bom

Tashin Bom A Kaduna: Yadda Na Tsallake Rijiya Da Baya - Dattijo Mai Shekara 74

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

June 23, 2025
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

June 23, 2025
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.