ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Kaduna

Biyo bayan harin bam da aka kai kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, Gwamnatin tarayya za ta sake gina wa mazauna kauyen gidaje, Makaranta da Asibiti sannan kuma za ta samar musu da kayan Noma.

Shi ma, Gwamna Uba Sani ya baiwa iyalan wadanda lamarin ya rutsa da su tallafi, inda ya ce, gwamnati za ta dauki nauyin kudin duk abinda ake bukata wajen jinya ga wadanda suka jikkata kuma ake duba lafiyarsu a asibitin koyarwa na Barau Dikko da ke jihar Kaduna.

  • Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba
  • A Magance Rashin Aikin Yi A Tsakanin Matasa

Bugu da kari, Gwamnan ya sha alwashin bayar da tallafi na kudi, kula da lafiyar kwakwalwa da kayan masarufi ga marayun da suka rasa masu kula da su a wannan mummunan lamari.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da ya tarbi wata tawagar jiga-jigan gwamnatin tarayya da suka hada da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, kakakin majalisar wakilai Abbas Tajuddeen, ministan tsaro Mohammed Badaru Abubakar, da shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje.

Gwamna Sani ya kuma mika godiyarsa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta mika ta’aziyyarsa kan ibtila’in inda kuma ya bada umurnin gudanar da bincike cikin gaggawa don gano musabbabin kai harin.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Gwamnan ya kuma tabbatar wa da tawagar cewa, za a bayyanawa Jama’a sakamakon binciken da zarar an kammala, sannan ya jaddada kudirin Shugaba Tinubu na biyan diyya ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da kaddamar da sake gina muhimman ababen more rayuwa a cikin al’ummar Tudun Biri.

Acewarsa, “Za a gina gidaje na zamani tare da samar musu da asibiti da kayan noma da makarantu. Don haka, ina godiya ga shugaban kasa da mataimakinsa”, inji Gwamna Sani.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, wanda ya wakilci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya mika sakon jajensu tare da nuna goyon bayansu ga gwamnati da al’ummar Kaduna a wannan lokaci mai cike da damuwa.

Kaduna
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.