• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa gayyatar da shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai tafi birnin San Francisco na kasar Amurka cikin kwanaki masu zuwa, don ganawa da shugaba Biden, gami da halartar kwarya-kwaryar taro karo na 30 na shugabannin kasashe mambobin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasific (APEC). Wannan ziyara ce da shugaban na kasar Sin zai sake kai wa kasar Amurka, bayan wasu shekaru 6, kana sake ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi bayan shekara 1, wadda ke da ma’anar musamman.

Wani abun lura shi ne, wasu kwanaki da suka gabata, kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra ta kasar Amurka ta zo kasar Sin don halartar biki. Wannan kungiyar makada ita ce kungiyar makada ta kasar Amurka ta farko da ta ziyarci kasar Sin, bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, inda ta taimaka wajen farfado da cudanyar kasashen Amurka da Sin a fannin al’adu. Daga nan, kungiyar ta ziyarci kasar Sin har sau 12, inda ta taka muhimmiyar rawa a kokarin kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2. Sai dai a wannan karo, shugaba Xi Jinping ya amsa wata wasika ta shugaban kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra Matias Tarnopolsky, inda ya ce, yana fatan ganin makadan kungiyar sun hada gwiwa tare da takwarorinsu na kasar Sin, da na sauran kasashe, don karfafa cudanya, da raya fasahohi na al’adu, ta yadda za a ci gaba da tabbatar da cudanyar kasashen Sin da Amurka a fannin al’adu, da kasancewar zumunta tsakanin al’ummun kasashe daban daban. Wasikar shugaba Xi ta nuna yadda ake son karfafa cudanya da zumunta tsakanin Sin da Amurka, wadda ta nuna wani yanayi mai yakini kan ganawar shugabannin kasashen Sin da Amurka.

  • Kade-Kaden Symphony Ta Philadelphia Na Ba Da Gudummawa Waje Inganta Abokantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Ana Begen Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Birnin San Francisco

A dayan bangare kuma, mu’ammalar gwamnatocin Sin da Amurka ita ma ta samu ci gaba mai armashi a kwanakin nan. Bisa gayyatar da ministar kudi ta kasar Amurka Janet Yellen ta yi, He Lifeng, mataimakin fitaministan kasar Sin, wanda ke jagorantar aikin musayar ra’ayi tare da bangaren Amurka ta fuskar tattalin arziki da ciniki, ya ziyarci kasar Amurka tsakanin ranar 8 zuwa ta 12 ga watan Nuwamban da muke ciki, inda ya tattauna tare da Madam Yellen, gami da cimma matsaya kan wasu batutuwa. Misali, kasashen 2 sun yarda da kara musayar ra’ayi da juna, don neman samun matsaya daya, da shawo kan bambancin ra’ayi. Kana sun jaddada cewa ba za su katse hulda a fannin tattalin arziki ba. Haka zalika, sun yarda da yin kokari tare don tinkarar wasu kalubaloli na bai daya, irinsu tabbatar da karuwar tattalin arziki, da samun wani yanayi mai karko a fannin hada-hadar kudi, da dai sauransu. Yadda aka cimma matsaya a wadannan fannoni shi ma ya nuna cewa an share fage sosai domin ganawar da za a yi tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka.

Da ma huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala, tun bayan da kasar Amurka ta fara takaita cinikin da take yi da kasar Sin bisa kashin kanta a shekarar 2018, lamarin da ya sa gamayyar kasa da kasa damuwa kan yiwuwar abkuwar “sabon yakin cacar baka”. Amma a hakika, matakan da kasar Amurka ta dauka ba su dace da moriyar jama’ar kasar ba, saboda babbar moriyar kasashen 2 a hade suke, wato suna bukatar juna. Wannan ya yi kama da maganar da Gavin Newsom, gwamnan jihar California ta kasar Amukra ya fada, yayin da yake ziyara a kasar Sin a kwanan baya, inda ya ce, “ Idan kasar Sin ta samu karin nasarori, to, mu ma za mu cimma karin nasarori. ”

Ban da haka, kasashen Sin da Amurka su ne masu tattalin arziki mafi girma a duniya, inda adadin tattalin arzikinsu ya zarce kashi 1 cikin kashi 3 na tattalin arzikin daukacin duniya. Saboda haka gwamayyar kasa da kasa na son ganin huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta koma cikin wani yanayi mai armashi, ta yadda za a iya samar da sauki ga mawuyacin halin da duniya ke ciki, da tabbatar da kwanciyar hankali, da ci gaban tattalin arzikin mabambantan kasashe. Ta hanyar ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi a wannan karo, ana sa ran ganin huldar dake tsakanin kasashen 2 ta inganta, lamarin da zai biya bukatun kasashen duniya.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Sai dai don cimma burin kyautata huldar dake tsakanin Sin da Amurka, ana bukatar kasar Amurka ta cika alkawarin da take dauka, maimakon yadda ta saba yi a baya, inda take fadin wani abu ga kasar Sin, amma ta aikata wani abu na daban daga bisani. Kamar yadda Gal Luft, darektan cibiyar nazarin aikin tsaro na duniya, ya fada: Karfafa cudanya tsakanin Sin da Amurka zai taimakawa daidaita huldarsu, domin ana bukatar aiwatar da sakamakon da aka cimma. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Joe BidenPutin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ziyarar Xi Ta APEC Na Nuni Da Kyakkyawar Sakamakon Yunkurin Daidata Dangantakar Sin Da Amurka

Next Post

Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta’addanci

Related

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

33 minutes ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

2 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

9 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

10 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

21 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

22 hours ago
Next Post
Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta’addanci

Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.