ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Bisa gayyatar da shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai tafi birnin San Francisco na kasar Amurka cikin kwanaki masu zuwa, don ganawa da shugaba Biden, gami da halartar kwarya-kwaryar taro karo na 30 na shugabannin kasashe mambobin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasific (APEC). Wannan ziyara ce da shugaban na kasar Sin zai sake kai wa kasar Amurka, bayan wasu shekaru 6, kana sake ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi bayan shekara 1, wadda ke da ma’anar musamman.

Wani abun lura shi ne, wasu kwanaki da suka gabata, kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra ta kasar Amurka ta zo kasar Sin don halartar biki. Wannan kungiyar makada ita ce kungiyar makada ta kasar Amurka ta farko da ta ziyarci kasar Sin, bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, inda ta taimaka wajen farfado da cudanyar kasashen Amurka da Sin a fannin al’adu. Daga nan, kungiyar ta ziyarci kasar Sin har sau 12, inda ta taka muhimmiyar rawa a kokarin kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2. Sai dai a wannan karo, shugaba Xi Jinping ya amsa wata wasika ta shugaban kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra Matias Tarnopolsky, inda ya ce, yana fatan ganin makadan kungiyar sun hada gwiwa tare da takwarorinsu na kasar Sin, da na sauran kasashe, don karfafa cudanya, da raya fasahohi na al’adu, ta yadda za a ci gaba da tabbatar da cudanyar kasashen Sin da Amurka a fannin al’adu, da kasancewar zumunta tsakanin al’ummun kasashe daban daban. Wasikar shugaba Xi ta nuna yadda ake son karfafa cudanya da zumunta tsakanin Sin da Amurka, wadda ta nuna wani yanayi mai yakini kan ganawar shugabannin kasashen Sin da Amurka.

  • Kade-Kaden Symphony Ta Philadelphia Na Ba Da Gudummawa Waje Inganta Abokantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Ana Begen Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Birnin San Francisco

A dayan bangare kuma, mu’ammalar gwamnatocin Sin da Amurka ita ma ta samu ci gaba mai armashi a kwanakin nan. Bisa gayyatar da ministar kudi ta kasar Amurka Janet Yellen ta yi, He Lifeng, mataimakin fitaministan kasar Sin, wanda ke jagorantar aikin musayar ra’ayi tare da bangaren Amurka ta fuskar tattalin arziki da ciniki, ya ziyarci kasar Amurka tsakanin ranar 8 zuwa ta 12 ga watan Nuwamban da muke ciki, inda ya tattauna tare da Madam Yellen, gami da cimma matsaya kan wasu batutuwa. Misali, kasashen 2 sun yarda da kara musayar ra’ayi da juna, don neman samun matsaya daya, da shawo kan bambancin ra’ayi. Kana sun jaddada cewa ba za su katse hulda a fannin tattalin arziki ba. Haka zalika, sun yarda da yin kokari tare don tinkarar wasu kalubaloli na bai daya, irinsu tabbatar da karuwar tattalin arziki, da samun wani yanayi mai karko a fannin hada-hadar kudi, da dai sauransu. Yadda aka cimma matsaya a wadannan fannoni shi ma ya nuna cewa an share fage sosai domin ganawar da za a yi tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka.

ADVERTISEMENT

Da ma huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala, tun bayan da kasar Amurka ta fara takaita cinikin da take yi da kasar Sin bisa kashin kanta a shekarar 2018, lamarin da ya sa gamayyar kasa da kasa damuwa kan yiwuwar abkuwar “sabon yakin cacar baka”. Amma a hakika, matakan da kasar Amurka ta dauka ba su dace da moriyar jama’ar kasar ba, saboda babbar moriyar kasashen 2 a hade suke, wato suna bukatar juna. Wannan ya yi kama da maganar da Gavin Newsom, gwamnan jihar California ta kasar Amukra ya fada, yayin da yake ziyara a kasar Sin a kwanan baya, inda ya ce, “ Idan kasar Sin ta samu karin nasarori, to, mu ma za mu cimma karin nasarori. ”

Ban da haka, kasashen Sin da Amurka su ne masu tattalin arziki mafi girma a duniya, inda adadin tattalin arzikinsu ya zarce kashi 1 cikin kashi 3 na tattalin arzikin daukacin duniya. Saboda haka gwamayyar kasa da kasa na son ganin huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta koma cikin wani yanayi mai armashi, ta yadda za a iya samar da sauki ga mawuyacin halin da duniya ke ciki, da tabbatar da kwanciyar hankali, da ci gaban tattalin arzikin mabambantan kasashe. Ta hanyar ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi a wannan karo, ana sa ran ganin huldar dake tsakanin kasashen 2 ta inganta, lamarin da zai biya bukatun kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Sai dai don cimma burin kyautata huldar dake tsakanin Sin da Amurka, ana bukatar kasar Amurka ta cika alkawarin da take dauka, maimakon yadda ta saba yi a baya, inda take fadin wani abu ga kasar Sin, amma ta aikata wani abu na daban daga bisani. Kamar yadda Gal Luft, darektan cibiyar nazarin aikin tsaro na duniya, ya fada: Karfafa cudanya tsakanin Sin da Amurka zai taimakawa daidaita huldarsu, domin ana bukatar aiwatar da sakamakon da aka cimma. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta’addanci

Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.