ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Za Ta Iya Amfanin Duniya

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Bisa gayyatar da shugaban kasar Amurka Joe Biden ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai tafi birnin San Francisco na kasar Amurka cikin kwanaki masu zuwa, don ganawa da shugaba Biden, gami da halartar kwarya-kwaryar taro karo na 30 na shugabannin kasashe mambobin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasific (APEC). Wannan ziyara ce da shugaban na kasar Sin zai sake kai wa kasar Amurka, bayan wasu shekaru 6, kana sake ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi bayan shekara 1, wadda ke da ma’anar musamman.

Wani abun lura shi ne, wasu kwanaki da suka gabata, kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra ta kasar Amurka ta zo kasar Sin don halartar biki. Wannan kungiyar makada ita ce kungiyar makada ta kasar Amurka ta farko da ta ziyarci kasar Sin, bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, inda ta taimaka wajen farfado da cudanyar kasashen Amurka da Sin a fannin al’adu. Daga nan, kungiyar ta ziyarci kasar Sin har sau 12, inda ta taka muhimmiyar rawa a kokarin kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2. Sai dai a wannan karo, shugaba Xi Jinping ya amsa wata wasika ta shugaban kungiyar makada ta Philadelphia Orchestra Matias Tarnopolsky, inda ya ce, yana fatan ganin makadan kungiyar sun hada gwiwa tare da takwarorinsu na kasar Sin, da na sauran kasashe, don karfafa cudanya, da raya fasahohi na al’adu, ta yadda za a ci gaba da tabbatar da cudanyar kasashen Sin da Amurka a fannin al’adu, da kasancewar zumunta tsakanin al’ummun kasashe daban daban. Wasikar shugaba Xi ta nuna yadda ake son karfafa cudanya da zumunta tsakanin Sin da Amurka, wadda ta nuna wani yanayi mai yakini kan ganawar shugabannin kasashen Sin da Amurka.

  • Kade-Kaden Symphony Ta Philadelphia Na Ba Da Gudummawa Waje Inganta Abokantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
  • Ana Begen Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka A Birnin San Francisco

A dayan bangare kuma, mu’ammalar gwamnatocin Sin da Amurka ita ma ta samu ci gaba mai armashi a kwanakin nan. Bisa gayyatar da ministar kudi ta kasar Amurka Janet Yellen ta yi, He Lifeng, mataimakin fitaministan kasar Sin, wanda ke jagorantar aikin musayar ra’ayi tare da bangaren Amurka ta fuskar tattalin arziki da ciniki, ya ziyarci kasar Amurka tsakanin ranar 8 zuwa ta 12 ga watan Nuwamban da muke ciki, inda ya tattauna tare da Madam Yellen, gami da cimma matsaya kan wasu batutuwa. Misali, kasashen 2 sun yarda da kara musayar ra’ayi da juna, don neman samun matsaya daya, da shawo kan bambancin ra’ayi. Kana sun jaddada cewa ba za su katse hulda a fannin tattalin arziki ba. Haka zalika, sun yarda da yin kokari tare don tinkarar wasu kalubaloli na bai daya, irinsu tabbatar da karuwar tattalin arziki, da samun wani yanayi mai karko a fannin hada-hadar kudi, da dai sauransu. Yadda aka cimma matsaya a wadannan fannoni shi ma ya nuna cewa an share fage sosai domin ganawar da za a yi tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka.

ADVERTISEMENT

Da ma huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta gamu da matsala, tun bayan da kasar Amurka ta fara takaita cinikin da take yi da kasar Sin bisa kashin kanta a shekarar 2018, lamarin da ya sa gamayyar kasa da kasa damuwa kan yiwuwar abkuwar “sabon yakin cacar baka”. Amma a hakika, matakan da kasar Amurka ta dauka ba su dace da moriyar jama’ar kasar ba, saboda babbar moriyar kasashen 2 a hade suke, wato suna bukatar juna. Wannan ya yi kama da maganar da Gavin Newsom, gwamnan jihar California ta kasar Amukra ya fada, yayin da yake ziyara a kasar Sin a kwanan baya, inda ya ce, “ Idan kasar Sin ta samu karin nasarori, to, mu ma za mu cimma karin nasarori. ”

Ban da haka, kasashen Sin da Amurka su ne masu tattalin arziki mafi girma a duniya, inda adadin tattalin arzikinsu ya zarce kashi 1 cikin kashi 3 na tattalin arzikin daukacin duniya. Saboda haka gwamayyar kasa da kasa na son ganin huldar dake tsakanin Sin da Amurka ta koma cikin wani yanayi mai armashi, ta yadda za a iya samar da sauki ga mawuyacin halin da duniya ke ciki, da tabbatar da kwanciyar hankali, da ci gaban tattalin arzikin mabambantan kasashe. Ta hanyar ganawar da shugabannin Sin da Amurka za su yi a wannan karo, ana sa ran ganin huldar dake tsakanin kasashen 2 ta inganta, lamarin da zai biya bukatun kasashen duniya.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Sai dai don cimma burin kyautata huldar dake tsakanin Sin da Amurka, ana bukatar kasar Amurka ta cika alkawarin da take dauka, maimakon yadda ta saba yi a baya, inda take fadin wani abu ga kasar Sin, amma ta aikata wani abu na daban daga bisani. Kamar yadda Gal Luft, darektan cibiyar nazarin aikin tsaro na duniya, ya fada: Karfafa cudanya tsakanin Sin da Amurka zai taimakawa daidaita huldarsu, domin ana bukatar aiwatar da sakamakon da aka cimma. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta’addanci

Nuhu Ribadu Ya Yaba Wa Sojoji Kan Nasarar Da Ake Samu A Yaki Da Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.