• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Labarai
0
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje na kara shan matsin lamba a kan ya sauka daga mukaminsa, inda wani jigon APC, Alhaji Saleh Zazzaga ya rubuta masa wasika tare da ba shi wa’adin kwanaki 7 ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC.

Alhaji Zazzaga, ya kasance shugaban kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar APC na yankin arewa ta tsakiya, sannan kuma shi mamba ne a lokacin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, ya dai bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Majalisa Ta Amince Jami’an Kiyaye HaÉ—urra Su RiÆ™e Bindiga 

Ya ce a cikin wasikar da ya rubuta akwai dalilansa wanda ya bukaci Ganduje ya yi murabus tare da bayar da wa’adin kwanaki 7 da zai kare a ranar Litinin na mako mai zuwa, wanda ya ce zai dauki matakin shari’a.

A cewarsa, a babban taron jam’iyyar da aka gudanar da ranar 26 ga Maris, 2022, ya kamata a zabi dan yankin arewa ta tsakiya ne ba Ganduje da ya fito daga yankin arewa maso yamma ba.

Jigon jam’iyyar APC ya ce kasancewar Ganduje shugaban jam’iyyar hakan ya saba wa sashi na 31.5 31.5 (i) da (ib) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC na shekara 2022 wanda aka yi wa garanbawul, sannan kuma ya saba wa yarjejeniyar tsarin karba-karba na mukamin shugabancin jam’iyyar wanda ya kamata a bai wa yankin arewa ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Ya ce wasikar tana zama wani shaida na hanyar warware rikici cikin sauki da kuma tattaunawa ta lumana, amma duk da haka Ganduje ya yi kememe ya ci gaba da zama kan mukamin da ya kamata a bai wad an asalin yankin arewa ta tsakiya.

Haka kuma Zazzaga ya yi kwafin wasikar ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da shugaban majalisar wakilai, Honorabul Tajudeen Abbas da kwamitin gudanarwa na APC na kasa da kuma sashin shari’a na jam’iyyar APC.

Idan za a iya tunawa dai, kungiyar APC na yankin arewa ta tsakiya sun gurfanar da Ganduje a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja na neman a tsige shi daga kan mukaminsa na shugaban jam’iyyar, sai dai kotun ta yi watsi da karar sakamakon wasu dalilai.

Sai dai kuma, ‘ya’yan jam’iyyar APC a yankin arewa ta tsakiya da sauran wasu jiga-jigan jam’iyyar daga yankin sun ci gaba da wannan yaki har sai hakarsu ta cimma ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGandujeMatsin LambaMulkiShugabanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

Next Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Related

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

1 hour ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

2 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

3 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

15 hours ago
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.