• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
in Labarai
0
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje na kara shan matsin lamba a kan ya sauka daga mukaminsa, inda wani jigon APC, Alhaji Saleh Zazzaga ya rubuta masa wasika tare da ba shi wa’adin kwanaki 7 ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC.

Alhaji Zazzaga, ya kasance shugaban kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar APC na yankin arewa ta tsakiya, sannan kuma shi mamba ne a lokacin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, ya dai bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Majalisa Ta Amince Jami’an Kiyaye Haɗurra Su Riƙe Bindiga 

Ya ce a cikin wasikar da ya rubuta akwai dalilansa wanda ya bukaci Ganduje ya yi murabus tare da bayar da wa’adin kwanaki 7 da zai kare a ranar Litinin na mako mai zuwa, wanda ya ce zai dauki matakin shari’a.

A cewarsa, a babban taron jam’iyyar da aka gudanar da ranar 26 ga Maris, 2022, ya kamata a zabi dan yankin arewa ta tsakiya ne ba Ganduje da ya fito daga yankin arewa maso yamma ba.

Jigon jam’iyyar APC ya ce kasancewar Ganduje shugaban jam’iyyar hakan ya saba wa sashi na 31.5 31.5 (i) da (ib) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC na shekara 2022 wanda aka yi wa garanbawul, sannan kuma ya saba wa yarjejeniyar tsarin karba-karba na mukamin shugabancin jam’iyyar wanda ya kamata a bai wa yankin arewa ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ya ce wasikar tana zama wani shaida na hanyar warware rikici cikin sauki da kuma tattaunawa ta lumana, amma duk da haka Ganduje ya yi kememe ya ci gaba da zama kan mukamin da ya kamata a bai wad an asalin yankin arewa ta tsakiya.

Haka kuma Zazzaga ya yi kwafin wasikar ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da shugaban majalisar wakilai, Honorabul Tajudeen Abbas da kwamitin gudanarwa na APC na kasa da kuma sashin shari’a na jam’iyyar APC.

Idan za a iya tunawa dai, kungiyar APC na yankin arewa ta tsakiya sun gurfanar da Ganduje a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja na neman a tsige shi daga kan mukaminsa na shugaban jam’iyyar, sai dai kotun ta yi watsi da karar sakamakon wasu dalilai.

Sai dai kuma, ‘ya’yan jam’iyyar APC a yankin arewa ta tsakiya da sauran wasu jiga-jigan jam’iyyar daga yankin sun ci gaba da wannan yaki har sai hakarsu ta cimma ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGandujeMatsin LambaMulkiShugabanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

Next Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Related

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Labarai

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

16 minutes ago
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Labarai

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

2 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

3 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

4 hours ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

16 hours ago
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano
Labarai

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

18 hours ago
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.