• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje na kara shan matsin lamba a kan ya sauka daga mukaminsa, inda wani jigon APC, Alhaji Saleh Zazzaga ya rubuta masa wasika tare da ba shi wa’adin kwanaki 7 ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC.

Alhaji Zazzaga, ya kasance shugaban kungiyar ‘ya’yan jam’iyyar APC na yankin arewa ta tsakiya, sannan kuma shi mamba ne a lokacin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, ya dai bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Majalisa Ta Amince Jami’an Kiyaye Haɗurra Su Riƙe Bindiga 

Ya ce a cikin wasikar da ya rubuta akwai dalilansa wanda ya bukaci Ganduje ya yi murabus tare da bayar da wa’adin kwanaki 7 da zai kare a ranar Litinin na mako mai zuwa, wanda ya ce zai dauki matakin shari’a.

A cewarsa, a babban taron jam’iyyar da aka gudanar da ranar 26 ga Maris, 2022, ya kamata a zabi dan yankin arewa ta tsakiya ne ba Ganduje da ya fito daga yankin arewa maso yamma ba.

Jigon jam’iyyar APC ya ce kasancewar Ganduje shugaban jam’iyyar hakan ya saba wa sashi na 31.5 31.5 (i) da (ib) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC na shekara 2022 wanda aka yi wa garanbawul, sannan kuma ya saba wa yarjejeniyar tsarin karba-karba na mukamin shugabancin jam’iyyar wanda ya kamata a bai wa yankin arewa ta tsakiya.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Ya ce wasikar tana zama wani shaida na hanyar warware rikici cikin sauki da kuma tattaunawa ta lumana, amma duk da haka Ganduje ya yi kememe ya ci gaba da zama kan mukamin da ya kamata a bai wad an asalin yankin arewa ta tsakiya.

Haka kuma Zazzaga ya yi kwafin wasikar ga Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio da shugaban majalisar wakilai, Honorabul Tajudeen Abbas da kwamitin gudanarwa na APC na kasa da kuma sashin shari’a na jam’iyyar APC.

Idan za a iya tunawa dai, kungiyar APC na yankin arewa ta tsakiya sun gurfanar da Ganduje a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja na neman a tsige shi daga kan mukaminsa na shugaban jam’iyyar, sai dai kotun ta yi watsi da karar sakamakon wasu dalilai.

Sai dai kuma, ‘ya’yan jam’iyyar APC a yankin arewa ta tsakiya da sauran wasu jiga-jigan jam’iyyar daga yankin sun ci gaba da wannan yaki har sai hakarsu ta cimma ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGandujeMatsin LambaMulkiShugabanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kokarin Farfado Da Ilimi: Gwamnan Kano Ya Zama Gwarzo A Tsakanin Gwamnoni

Next Post

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

14 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

17 hours ago
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Sake Nanata Ba Da Kariya Ga Kudaden Ajiya A Bankuna

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.