• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Yi Alhinin Rasuwar Darakta Aminu S. Bono

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Ganduje Ya Yi Alhinin Rasuwar Darakta Aminu S. Bono
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Dokta Abdullahi Ganduje ya yi alhinin rasuwar daraktan masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood, Aminu Surajo Bono.

A cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labaransa, Edwin Olofu, ya fitar a ranar Talata, Dokta Ganduje, ya ce ya kadu matuka bayan samu labarin rasuwar fitaccen Daraktan.

  • Zan Biya Wa Aminu S. Bono Duk Bashin Da Ake Bin Sa – Aisha Humaira
  • An Saki Fursunoni 4,000 Don Rage Cunkoso A Gidajen Yari A Nijeriya

Ganduje wanda ya ce rasuwar Darakta Aminu S. Bono ba kamaramin rashi ba ne ga masana’antar Kannywood, inda ya kara da cewa rasuwar daraktan ta bar babban gibi a masana’antar.

Shugaban jam’iyyar, ya kara da cewa Darakta Bono ya yi amfani da lokacinsa wajen bunkasa masana’antar Kannywood ta hanaya gudanar da tsaftacacciyar rayuwa.

Ganduje ya ce, “Na kadu matuka da samun labarin rasuwar Darakta Aminu Surajo Bono. Wannan ba rashi ba ne kawai ga masana’antar Kannywood ba. Babban rashi ne ga al’umma.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

“Ina amfani da wannan dama don mika ta’aziyya ga iyalansa da ‘yan uwansa da masana’antar Kannywood baki daya. Ina rokon Allah Ya ba su juriyar wannan rashi.

“Tabbas rayuwar Darakta Bono a cikin fina-finansa da kuma zahiri abar yabawa ce.”

Shugaban jam’iyyar, ya ce yana rokon Allah (SWT) da ya bai wa iyalansa da masana’antar kannywood juriyar wannan baban rashi, sannan ya roki Allah (SWT) da ya gafarta wa mamacin.

Da yammacin ranar Litinin ne Daraktan ya rasu, bayan ya dawo daga wajen aiki.

Rasuwarsa ta girgiza masana’antar Kannywood, inda abokan sana’arsa suka shiga yi masa addu’a da samun dacewar Allah SWT.

Da safiyar ranar Talata aka yi jana’izarsa a unguwarsu da ke Dandago a birnin Kano, sannan aka birne shi a makabartar Dandolo da ke Goron Dutse.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhiniAminu S BonoAPCFina-finan HausaGandujeKannywoodRasuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Saki Fursunoni 4,000 Don Rage Cunkoso A Gidajen Yari A Nijeriya

Next Post

Zaben Nasarawa: ‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaro Gabanin Hukuncin Kotun Daukaka Kara 

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

49 minutes ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

3 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

4 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

12 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

13 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

14 hours ago
Next Post
Zaben Nasarawa: ‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaro Gabanin Hukuncin Kotun Daukaka Kara 

Zaben Nasarawa: 'Yansanda Sun Tsaurara Tsaro Gabanin Hukuncin Kotun Daukaka Kara 

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.