• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
12 months ago
in Labarai
0
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Gobir na Gatawa, Alhaji Isa Muhammad Bawa da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da shi ya bukaci taimakon Gwamnatin Jihar Sakkwato, domin kubutar da shi daga hannunsu. 

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da tsohon Sarkin Daular Gobir da ke Sabon- Birni tare da dansa kusan makonni uku a kwanar Maharba da ke a Goronyo a kan hanyarsa ta komawa gida Sabon- Birni daga Sakkwato, inda suka rika harbi ba kakkautawa wanda ya tilastawa motarsa tsayawa.

  • Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara
  • Shugabannin SADC Za Su Hallara A Sabon Ginin Ofishin Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa Domin Gudanar Da Taron Shekara

‘Yan ta’adda na cin karensu ba babbaka a Gabascin Sakkwato da ke da kananan hukumomi shida, inda suke kisan gilla, garkuwa da mutane, satar shanu, mayar da garuruwa kufai da tilastawa al’umma kaurace wa gona.

Da farko ‘yan ta’addan sun bukaci a biya kudin fansar Sarkin Naira biliyan daya, amma daga baya suka rage kudin zuwa Naira miliyan 500.

A wani faifan bidiyon na minti daya da ‘yan ta’addan suka saki a ranar Asabar wanda aka dauka a ranar Laraba, an nuno Sarkin cikin daji a cikin mummunan yanayi da zubar jini a rigarsa yana cewar yana jin jiki kuma gwamnatin Sakkwato ba ta taimake shi ba.

Labarai Masu Nasaba

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

“Ina rokon ‘yan uwana da masoyana da abokaina da shugabanni na cewar an kai rana ta karshe yau Laraba, don haka ina so su taimake ni. Ina sanar da su cewar wallahi, wallahi mutanen nan sun ma gaji da mu don duk abin da ake yi sun yi amma gwamnatinmu ba ta taimake ni ba, kuma ina ganin duk halin dana shiga a duniya za ta taimake ni amma ba ta taimake ni ba.”

“Ni ma’aikacin gwamnati ne shekara da shekaru ina bauta mata, na yi shekaru 45 ina bautawa gwamnati kuma duk a aikin sarauta.” cewar Sarkin wanda ba a nuno fuskar ‘yan bindigar da ke yi masa bidiyo da tambayoyi ba.

Sarkin na Gatawa ya rasa rawaninsa na babbar sarautar Sarkin Gobir na Sabon- Birni wadda ke da dadadden tarihi a watan Afrilu a yayin da gwamnatin Sakkwato ta tube rawanin Sarakuna 15 tare da sauyawa wasu masarautu.

An rage masa girma tare da mayar da shi Sarkin Gatawa, masarautar da ke karkashin ikonsa

Jim kadan da garkuwa da Sarkin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan, Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewar suna kan gudanar da bincike kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GarkuwaSakkwatoSarkiYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara

Next Post

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

Related

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

32 minutes ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

2 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

4 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

5 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

5 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

6 hours ago
Next Post
PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.