• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
in Labarai
0
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Gobir na Gatawa, Alhaji Isa Muhammad Bawa da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da shi ya bukaci taimakon Gwamnatin Jihar Sakkwato, domin kubutar da shi daga hannunsu. 

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da tsohon Sarkin Daular Gobir da ke Sabon- Birni tare da dansa kusan makonni uku a kwanar Maharba da ke a Goronyo a kan hanyarsa ta komawa gida Sabon- Birni daga Sakkwato, inda suka rika harbi ba kakkautawa wanda ya tilastawa motarsa tsayawa.

  • Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara
  • Shugabannin SADC Za Su Hallara A Sabon Ginin Ofishin Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa Domin Gudanar Da Taron Shekara

‘Yan ta’adda na cin karensu ba babbaka a Gabascin Sakkwato da ke da kananan hukumomi shida, inda suke kisan gilla, garkuwa da mutane, satar shanu, mayar da garuruwa kufai da tilastawa al’umma kaurace wa gona.

Da farko ‘yan ta’addan sun bukaci a biya kudin fansar Sarkin Naira biliyan daya, amma daga baya suka rage kudin zuwa Naira miliyan 500.

A wani faifan bidiyon na minti daya da ‘yan ta’addan suka saki a ranar Asabar wanda aka dauka a ranar Laraba, an nuno Sarkin cikin daji a cikin mummunan yanayi da zubar jini a rigarsa yana cewar yana jin jiki kuma gwamnatin Sakkwato ba ta taimake shi ba.

Labarai Masu Nasaba

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

“Ina rokon ‘yan uwana da masoyana da abokaina da shugabanni na cewar an kai rana ta karshe yau Laraba, don haka ina so su taimake ni. Ina sanar da su cewar wallahi, wallahi mutanen nan sun ma gaji da mu don duk abin da ake yi sun yi amma gwamnatinmu ba ta taimake ni ba, kuma ina ganin duk halin dana shiga a duniya za ta taimake ni amma ba ta taimake ni ba.”

“Ni ma’aikacin gwamnati ne shekara da shekaru ina bauta mata, na yi shekaru 45 ina bautawa gwamnati kuma duk a aikin sarauta.” cewar Sarkin wanda ba a nuno fuskar ‘yan bindigar da ke yi masa bidiyo da tambayoyi ba.

Sarkin na Gatawa ya rasa rawaninsa na babbar sarautar Sarkin Gobir na Sabon- Birni wadda ke da dadadden tarihi a watan Afrilu a yayin da gwamnatin Sakkwato ta tube rawanin Sarakuna 15 tare da sauyawa wasu masarautu.

An rage masa girma tare da mayar da shi Sarkin Gatawa, masarautar da ke karkashin ikonsa

Jim kadan da garkuwa da Sarkin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan, Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewar suna kan gudanar da bincike kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GarkuwaSakkwatoSarkiYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara

Next Post

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

Related

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

3 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

6 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

14 hours ago
Tinubu
Labarai

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

15 hours ago
Next Post
PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.