• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
Sarkin

Sarkin Gobir na Gatawa, Alhaji Isa Muhammad Bawa da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da shi ya bukaci taimakon Gwamnatin Jihar Sakkwato, domin kubutar da shi daga hannunsu. 

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da tsohon Sarkin Daular Gobir da ke Sabon- Birni tare da dansa kusan makonni uku a kwanar Maharba da ke a Goronyo a kan hanyarsa ta komawa gida Sabon- Birni daga Sakkwato, inda suka rika harbi ba kakkautawa wanda ya tilastawa motarsa tsayawa.

  • Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara
  • Shugabannin SADC Za Su Hallara A Sabon Ginin Ofishin Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa Domin Gudanar Da Taron Shekara

‘Yan ta’adda na cin karensu ba babbaka a Gabascin Sakkwato da ke da kananan hukumomi shida, inda suke kisan gilla, garkuwa da mutane, satar shanu, mayar da garuruwa kufai da tilastawa al’umma kaurace wa gona.

Da farko ‘yan ta’addan sun bukaci a biya kudin fansar Sarkin Naira biliyan daya, amma daga baya suka rage kudin zuwa Naira miliyan 500.

A wani faifan bidiyon na minti daya da ‘yan ta’addan suka saki a ranar Asabar wanda aka dauka a ranar Laraba, an nuno Sarkin cikin daji a cikin mummunan yanayi da zubar jini a rigarsa yana cewar yana jin jiki kuma gwamnatin Sakkwato ba ta taimake shi ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

“Ina rokon ‘yan uwana da masoyana da abokaina da shugabanni na cewar an kai rana ta karshe yau Laraba, don haka ina so su taimake ni. Ina sanar da su cewar wallahi, wallahi mutanen nan sun ma gaji da mu don duk abin da ake yi sun yi amma gwamnatinmu ba ta taimake ni ba, kuma ina ganin duk halin dana shiga a duniya za ta taimake ni amma ba ta taimake ni ba.”

“Ni ma’aikacin gwamnati ne shekara da shekaru ina bauta mata, na yi shekaru 45 ina bautawa gwamnati kuma duk a aikin sarauta.” cewar Sarkin wanda ba a nuno fuskar ‘yan bindigar da ke yi masa bidiyo da tambayoyi ba.

Sarkin na Gatawa ya rasa rawaninsa na babbar sarautar Sarkin Gobir na Sabon- Birni wadda ke da dadadden tarihi a watan Afrilu a yayin da gwamnatin Sakkwato ta tube rawanin Sarakuna 15 tare da sauyawa wasu masarautu.

An rage masa girma tare da mayar da shi Sarkin Gatawa, masarautar da ke karkashin ikonsa

Jim kadan da garkuwa da Sarkin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan, Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewar suna kan gudanar da bincike kan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu
Manyan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole
Labarai

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Next Post
PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.