ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Sarkin

Sarkin Gobir na Gatawa, Alhaji Isa Muhammad Bawa da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da shi ya bukaci taimakon Gwamnatin Jihar Sakkwato, domin kubutar da shi daga hannunsu. 

‘Yan ta’addan sun yi garkuwa da tsohon Sarkin Daular Gobir da ke Sabon- Birni tare da dansa kusan makonni uku a kwanar Maharba da ke a Goronyo a kan hanyarsa ta komawa gida Sabon- Birni daga Sakkwato, inda suka rika harbi ba kakkautawa wanda ya tilastawa motarsa tsayawa.

  • Hadin Gasasshen Burodi Da Kwai Da Madara
  • Shugabannin SADC Za Su Hallara A Sabon Ginin Ofishin Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa Domin Gudanar Da Taron Shekara

‘Yan ta’adda na cin karensu ba babbaka a Gabascin Sakkwato da ke da kananan hukumomi shida, inda suke kisan gilla, garkuwa da mutane, satar shanu, mayar da garuruwa kufai da tilastawa al’umma kaurace wa gona.

ADVERTISEMENT

Da farko ‘yan ta’addan sun bukaci a biya kudin fansar Sarkin Naira biliyan daya, amma daga baya suka rage kudin zuwa Naira miliyan 500.

A wani faifan bidiyon na minti daya da ‘yan ta’addan suka saki a ranar Asabar wanda aka dauka a ranar Laraba, an nuno Sarkin cikin daji a cikin mummunan yanayi da zubar jini a rigarsa yana cewar yana jin jiki kuma gwamnatin Sakkwato ba ta taimake shi ba.

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Ɗan Nijeriya Da Zai Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

“Ina rokon ‘yan uwana da masoyana da abokaina da shugabanni na cewar an kai rana ta karshe yau Laraba, don haka ina so su taimake ni. Ina sanar da su cewar wallahi, wallahi mutanen nan sun ma gaji da mu don duk abin da ake yi sun yi amma gwamnatinmu ba ta taimake ni ba, kuma ina ganin duk halin dana shiga a duniya za ta taimake ni amma ba ta taimake ni ba.”

“Ni ma’aikacin gwamnati ne shekara da shekaru ina bauta mata, na yi shekaru 45 ina bautawa gwamnati kuma duk a aikin sarauta.” cewar Sarkin wanda ba a nuno fuskar ‘yan bindigar da ke yi masa bidiyo da tambayoyi ba.

Sarkin na Gatawa ya rasa rawaninsa na babbar sarautar Sarkin Gobir na Sabon- Birni wadda ke da dadadden tarihi a watan Afrilu a yayin da gwamnatin Sakkwato ta tube rawanin Sarakuna 15 tare da sauyawa wasu masarautu.

An rage masa girma tare da mayar da shi Sarkin Gatawa, masarautar da ke karkashin ikonsa

Jim kadan da garkuwa da Sarkin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan, Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewar suna kan gudanar da bincike kan lamarin.

Sarkin
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa
Labarai

Babu Wani Ɗan Nijeriya Da Zai Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 28, 2026
Ruwa
Manyan Labarai

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano
Manyan Labarai

Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano

July 28, 2026
Next Post
PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

PDP Ta Lashe Zaɓen Shugabanin Ƙananan Hukumomin Bauchi Gaba Ɗaya

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Ƙosai: Remi Tinubu Ta Yi Kira ga Burna Boy da Davido Su Taimaka wa Talakawa

Babu Wani Ɗan Nijeriya Da Zai Kwana da Yunwa — Remi Tinubu

July 28, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Soke Umarnin Cire Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu Huɗu

July 28, 2026
Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

Kayayyaki Masu Fasahar AI Sun Zamo Sabbin Abubuwa Masu Tasiri A Cinikin Waje Na Kasar Sin

July 28, 2026
Ruwa

2027: Gwamnan Kaduna Ya Sanar Da Sabon Mataimakinsa A Zaɓen Gwamna

July 28, 2026
Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

Xi Jinping Ya Yi Bayani Kan Ayyuka Masu Nasaba Da Sinawan Dake Ketare

July 28, 2026
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Slovak A Beijing

July 28, 2026
Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano

Rimin-gado Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Batun Yi Wa ‘Yan Daba Alfarma A Kano

July 28, 2026
Wang Jian: Muna Fatan Mutanen Afirka Za Su Kara Cin Gajiyar Fasahar AI

Wang Jian: Muna Fatan Mutanen Afirka Za Su Kara Cin Gajiyar Fasahar AI

July 28, 2026
An Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwar Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka A Habasha

An Kaddamar Da Shirye-Shiryen Hadin Gwiwar Likitanci Tsakanin Sin Da Afirka A Habasha

July 28, 2026
Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

Peter Obi Ɗan Kasuwa Ne Don Haka Bai Dace Ya Zama Shugaban Ƙasa Ba – Oshiomhole

July 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.