• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarce shi ne da ya dawo da amana da gaskiya a aikin yaɗa labaran gwamnati ga jama’a.

Idris ya bayyana haka ne a Abuja a wajen bikin cika shekaru 60 da kafa Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Ƙasa (NIPR) a ranar Juma’a.

  • ‘Yan Kasuwar Nijeriya Za Su Haɗa Hannu Da Gwamnatin Kaduna Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Jihar
  • Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

A taron, mai taken “Hulɗa da Jama’a: Farfaɗo da Ƙima da Sauyin Tattalin Arziki”, ministan ya ce: “Shugaba na, Shugaba Bola Tinubu, wanda ya naɗa ni, ya amince in faɗi abubuwa yadda suke, amma cikin yanayi mai daɗi.

“Ya ba da umarnin cewa dole ne a dawo da amana ga aikin sadarwar jama’a.

“Hakan ne kawai mutane ko ’yan ƙasa za su mutunta kuma a ko yaushe su so sauraron gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

“Za mu ci gaba da yin hakan har zuwa ƙarshen aiki na a nan.”

A cewar ministan, yana da kyau a ko da yaushe a gaya wa jama’a gaskiya, su ma su gane cewa kana gaya masu gaskiya ne.

Ya ce: “Dole ne a dawo da amana da gaskiya a cikin aikin sadarwar jama’a.

“Don haka, idan ba ni da bayani game da wani abu, zan gwammace in rufe baki na, maimakon in faɗi abin ba daidai ba.”

Tsohuwar Mataimakiyar Shugaban Ƙasar Laberiya, Dakta Jewel Taylor, a cikin jawabin ta a taron, ta ba da labarin abin da ta fuskanta na ƙyama, suka, da canza labari da mugun tunanin mutane game da ita lokacin suna kan mulki.

Taylor ta yaba wa NIPR, inda ta ƙara da cewa rayuwar ‘yan siyasa ta ta’allaƙa ne kan magance rikice-rikice, don haka hulɗa da jama’a ya kasance makami mai inganci don tunkarar matsalolin.

Ta ƙara da cewa hulɗa da jama’a abu ne da ake yi a Afrika tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka inda ake amfani da ganguna daban-daban wajen sadar da saƙo ga jama’a.

Da yake karɓar baƙi a wajen taron, Shugaban hukumar ta NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya ce domin murnar zagayowar ranar, cibiyar ta dasa bishiyoyi 60 a kowace jiha a jihohi 36 na tarayyar ƙasar nan domin magance sauyin yanayi.

A cewar Neliaku, aikin hulɗa da jama’a na da matuƙar muhimmanci ga sake farfaɗo da ƙima da kuma sauyin tattalin arziki.

Ya jaddada ƙudirin cibiyar na samar da labari mai kyau ga Nijeriya.

Shi ma da yake jawabi, shugaban NIPR na farko, Mazi Okereke, ya ce abin da ya jawo wasu rikice-rikice a ƙasar nan shi ne taɓarɓarewar sadarwa tsakanin gwamnati da jama’a.

Ya ce: “Ya kamata gwamnatin Nijeriya ta sanya aikin hulɗa da jama’a a kan kujerar tuƙi. Mun ji daɗin cewa ɗaya daga cikin mu yanzu ya zama Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.”

A cikin saƙon sa na fatan alheri, Shugaban Gidan Talbijin na Ben TV da ke London, Mista Alistair Soyode, ya yi kira ga NIPR da ta kafa rassan ta a wasu ƙasashen duniya domin kula da ‘yan Nijeriya da ‘yan Afrika mazauna ƙasashen waje.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron ya jawo hankulan masu ruwa da tsaki daga gida da waje yayin da wasu fitattun mutane suka tattauna kan batun “yin amfani da hulɗa da jama’a don bunƙasar tattalin arziki”.

Haka kuma ya ruwaito cewa ɗaliban makarantar African International School da ke unguwar Asokoro a Abuja sun rera waƙar haɗin kai ta fitaccen mawaƙi Temi Dakolo a wurin taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaRahotanniSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Rangers Ta Lashe Gasar Firimiyar Nijeriya 

Next Post

Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

10 minutes ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

3 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

4 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

5 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
Next Post
Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya

Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.