ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Tsantsa Tinubu Ya Umarce Ni In Riƙa Faɗa – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarce shi ne da ya dawo da amana da gaskiya a aikin yaɗa labaran gwamnati ga jama’a.

Idris ya bayyana haka ne a Abuja a wajen bikin cika shekaru 60 da kafa Cibiyar Hulɗa da Jama’a ta Ƙasa (NIPR) a ranar Juma’a.

  • ‘Yan Kasuwar Nijeriya Za Su Haɗa Hannu Da Gwamnatin Kaduna Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Jihar
  • Za A Zuba Dala Miliyan 520 Don Habaka Noma A Jihohin Kudancin Nijeriya

A taron, mai taken “Hulɗa da Jama’a: Farfaɗo da Ƙima da Sauyin Tattalin Arziki”, ministan ya ce: “Shugaba na, Shugaba Bola Tinubu, wanda ya naɗa ni, ya amince in faɗi abubuwa yadda suke, amma cikin yanayi mai daɗi.

ADVERTISEMENT

“Ya ba da umarnin cewa dole ne a dawo da amana ga aikin sadarwar jama’a.

“Hakan ne kawai mutane ko ’yan ƙasa za su mutunta kuma a ko yaushe su so sauraron gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

“Za mu ci gaba da yin hakan har zuwa ƙarshen aiki na a nan.”

A cewar ministan, yana da kyau a ko da yaushe a gaya wa jama’a gaskiya, su ma su gane cewa kana gaya masu gaskiya ne.

Ya ce: “Dole ne a dawo da amana da gaskiya a cikin aikin sadarwar jama’a.

“Don haka, idan ba ni da bayani game da wani abu, zan gwammace in rufe baki na, maimakon in faɗi abin ba daidai ba.”

Tsohuwar Mataimakiyar Shugaban Ƙasar Laberiya, Dakta Jewel Taylor, a cikin jawabin ta a taron, ta ba da labarin abin da ta fuskanta na ƙyama, suka, da canza labari da mugun tunanin mutane game da ita lokacin suna kan mulki.

Taylor ta yaba wa NIPR, inda ta ƙara da cewa rayuwar ‘yan siyasa ta ta’allaƙa ne kan magance rikice-rikice, don haka hulɗa da jama’a ya kasance makami mai inganci don tunkarar matsalolin.

Ta ƙara da cewa hulɗa da jama’a abu ne da ake yi a Afrika tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka inda ake amfani da ganguna daban-daban wajen sadar da saƙo ga jama’a.

Da yake karɓar baƙi a wajen taron, Shugaban hukumar ta NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya ce domin murnar zagayowar ranar, cibiyar ta dasa bishiyoyi 60 a kowace jiha a jihohi 36 na tarayyar ƙasar nan domin magance sauyin yanayi.

A cewar Neliaku, aikin hulɗa da jama’a na da matuƙar muhimmanci ga sake farfaɗo da ƙima da kuma sauyin tattalin arziki.

Ya jaddada ƙudirin cibiyar na samar da labari mai kyau ga Nijeriya.

Shi ma da yake jawabi, shugaban NIPR na farko, Mazi Okereke, ya ce abin da ya jawo wasu rikice-rikice a ƙasar nan shi ne taɓarɓarewar sadarwa tsakanin gwamnati da jama’a.

Ya ce: “Ya kamata gwamnatin Nijeriya ta sanya aikin hulɗa da jama’a a kan kujerar tuƙi. Mun ji daɗin cewa ɗaya daga cikin mu yanzu ya zama Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.”

A cikin saƙon sa na fatan alheri, Shugaban Gidan Talbijin na Ben TV da ke London, Mista Alistair Soyode, ya yi kira ga NIPR da ta kafa rassan ta a wasu ƙasashen duniya domin kula da ‘yan Nijeriya da ‘yan Afrika mazauna ƙasashen waje.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa taron ya jawo hankulan masu ruwa da tsaki daga gida da waje yayin da wasu fitattun mutane suka tattauna kan batun “yin amfani da hulɗa da jama’a don bunƙasar tattalin arziki”.

Haka kuma ya ruwaito cewa ɗaliban makarantar African International School da ke unguwar Asokoro a Abuja sun rera waƙar haɗin kai ta fitaccen mawaƙi Temi Dakolo a wurin taron.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya

Lamarin Fanshon Tsofaffin Shugabanni A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.