• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

NIS Ta Samu Lambar Yabo Daga Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta karbu kyautar Naira miliyan 500 daga Gidauniyar Raya Afirka ta Abdulsamad Rabi’u, wadda ta ke taimakawa don tsaro da inganta rayuwar al’umma.

Kungiyar ta bayar da tallafin ne domin karfafa wa hukumar guiwa kan irin nasarorin da ta cimma wajen kyautata tsaro a bangaren shige da fice a Nijeriya da kuma matakin kasa da kasa.

  • Cutar Murar Tsuntsaye Ta Barke A Jihohi 28 – Gwamnatin Tarayya
  • ‘Yansanda Sun Kwato Makamai Da Dala 255,000 A Kwara

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwar da DCI Tony Akuneme, kakakin NIS, ya fitar a ranar Juma’a.

Sanarwar ta kara da cewa, a wani taron amsar wasikar tallafin da aka shirya a hedikwatar hukumar da ke Abuja, Kwanturolan hukumar, Isah Jere Idris, ya jinjina tare da yaba wa shugaban rukunin kamfanin BUA, Alhaji Abdulsamad Rabi’u bisa tallafin da kuma ganin irin kwazon ayyukan hukumar.

Ya jaddada aniyar hukumar na kara azama wajen inganta tsaro a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

NIS
Jagoran Gidauniyar Abdulsamad, Ubon Udoh yayin da ya ke mika shaidar tallafin

Ya kuma tabbatar da cewar tawagar za su yi amfani da kudaden ta hanyoyin da suka dace domin kwalliya ta ci gaba da biyan kudin sabulu.

An samar da gidauniyar ne a ne domin taimaka wa da karfafa bangaren tsaro da inganta ci gaban kasashen Afirka.

Hakan wani shiri ne na kokarin shugaban rukunin kamfanin BUA da ke yi wajen tabbatar da ingancin zaman lafiya da tsaro a kasashen Afrika tare kuma da bunkasa ci gaban al’ummar kasashen nahiyar.

Idan za a iya tunawa, duka a kokarin hukumar NIS a bangaren inganta aiki da kula da sashen shige da fice a 2022, Kwamitin Fadar Shugaban Kasa kan Harkokin Kasuwanci (PEBEC), ya karrama NIS da lambar yabo a matsayin hukumar da ta fi kwazo cikin ma’aikatun Gwamnatin Tarayya cikin watanni bakwai.

Jagoran Gidauniyar, ‘Abdul Samad Rabiu Initiative for Africa’, Ubon Udoh ne, ya jagoranci tawagar zuwa hedikwatar hukumar NIS domin mika kyautar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gidauniyar Abdulsamad RabiuIdris JereInganta TsaroKyautar KudiNISShige Da FiceTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cutar Murar Tsuntsaye Ta Barke A Jihohi 28 – Gwamnatin Tarayya

Next Post

An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

3 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

8 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

12 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

13 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.