ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

NIS Ta Samu Lambar Yabo Daga Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta karbu kyautar Naira miliyan 500 daga Gidauniyar Raya Afirka ta Abdulsamad Rabi’u, wadda ta ke taimakawa don tsaro da inganta rayuwar al’umma.

Kungiyar ta bayar da tallafin ne domin karfafa wa hukumar guiwa kan irin nasarorin da ta cimma wajen kyautata tsaro a bangaren shige da fice a Nijeriya da kuma matakin kasa da kasa.

  • Cutar Murar Tsuntsaye Ta Barke A Jihohi 28 – Gwamnatin Tarayya
  • ‘Yansanda Sun Kwato Makamai Da Dala 255,000 A Kwara

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwar da DCI Tony Akuneme, kakakin NIS, ya fitar a ranar Juma’a.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, a wani taron amsar wasikar tallafin da aka shirya a hedikwatar hukumar da ke Abuja, Kwanturolan hukumar, Isah Jere Idris, ya jinjina tare da yaba wa shugaban rukunin kamfanin BUA, Alhaji Abdulsamad Rabi’u bisa tallafin da kuma ganin irin kwazon ayyukan hukumar.

Ya jaddada aniyar hukumar na kara azama wajen inganta tsaro a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

NIS
Jagoran Gidauniyar Abdulsamad, Ubon Udoh yayin da ya ke mika shaidar tallafin

Ya kuma tabbatar da cewar tawagar za su yi amfani da kudaden ta hanyoyin da suka dace domin kwalliya ta ci gaba da biyan kudin sabulu.

An samar da gidauniyar ne a ne domin taimaka wa da karfafa bangaren tsaro da inganta ci gaban kasashen Afirka.

Hakan wani shiri ne na kokarin shugaban rukunin kamfanin BUA da ke yi wajen tabbatar da ingancin zaman lafiya da tsaro a kasashen Afrika tare kuma da bunkasa ci gaban al’ummar kasashen nahiyar.

Idan za a iya tunawa, duka a kokarin hukumar NIS a bangaren inganta aiki da kula da sashen shige da fice a 2022, Kwamitin Fadar Shugaban Kasa kan Harkokin Kasuwanci (PEBEC), ya karrama NIS da lambar yabo a matsayin hukumar da ta fi kwazo cikin ma’aikatun Gwamnatin Tarayya cikin watanni bakwai.

Jagoran Gidauniyar, ‘Abdul Samad Rabiu Initiative for Africa’, Ubon Udoh ne, ya jagoranci tawagar zuwa hedikwatar hukumar NIS domin mika kyautar.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

July 3, 2026
Next Post
An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

LABARAI MASU NASABA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.