ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Abdulsamad Ta Bai Wa Hukumar NIS Kyautar 500m Don Inganta Tsaro 

NIS Ta Samu Lambar Yabo Daga Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
NIS

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta karbu kyautar Naira miliyan 500 daga Gidauniyar Raya Afirka ta Abdulsamad Rabi’u, wadda ta ke taimakawa don tsaro da inganta rayuwar al’umma.

Kungiyar ta bayar da tallafin ne domin karfafa wa hukumar guiwa kan irin nasarorin da ta cimma wajen kyautata tsaro a bangaren shige da fice a Nijeriya da kuma matakin kasa da kasa.

  • Cutar Murar Tsuntsaye Ta Barke A Jihohi 28 – Gwamnatin Tarayya
  • ‘Yansanda Sun Kwato Makamai Da Dala 255,000 A Kwara

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwar da DCI Tony Akuneme, kakakin NIS, ya fitar a ranar Juma’a.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa, a wani taron amsar wasikar tallafin da aka shirya a hedikwatar hukumar da ke Abuja, Kwanturolan hukumar, Isah Jere Idris, ya jinjina tare da yaba wa shugaban rukunin kamfanin BUA, Alhaji Abdulsamad Rabi’u bisa tallafin da kuma ganin irin kwazon ayyukan hukumar.

Ya jaddada aniyar hukumar na kara azama wajen inganta tsaro a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

NIS
Jagoran Gidauniyar Abdulsamad, Ubon Udoh yayin da ya ke mika shaidar tallafin

Ya kuma tabbatar da cewar tawagar za su yi amfani da kudaden ta hanyoyin da suka dace domin kwalliya ta ci gaba da biyan kudin sabulu.

An samar da gidauniyar ne a ne domin taimaka wa da karfafa bangaren tsaro da inganta ci gaban kasashen Afirka.

Hakan wani shiri ne na kokarin shugaban rukunin kamfanin BUA da ke yi wajen tabbatar da ingancin zaman lafiya da tsaro a kasashen Afrika tare kuma da bunkasa ci gaban al’ummar kasashen nahiyar.

Idan za a iya tunawa, duka a kokarin hukumar NIS a bangaren inganta aiki da kula da sashen shige da fice a 2022, Kwamitin Fadar Shugaban Kasa kan Harkokin Kasuwanci (PEBEC), ya karrama NIS da lambar yabo a matsayin hukumar da ta fi kwazo cikin ma’aikatun Gwamnatin Tarayya cikin watanni bakwai.

Jagoran Gidauniyar, ‘Abdul Samad Rabiu Initiative for Africa’, Ubon Udoh ne, ya jagoranci tawagar zuwa hedikwatar hukumar NIS domin mika kyautar.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 24, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
Next Post
An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

An Yi Hasashen Tafiye-Tafiyen Fasinjoji A Bikin Bazara Na Sin Zai Karu Da Kashi 99.5

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.