• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla yara dari hudu, marayu da masu karamin karfi daga kananan hukumomi shida na jihar Kebbi ne suka samu tallafin karatu daga Gidauniyar M-TECH, ta hanyar ba su fom din JAMB kyauta tare da biyan dukkan kudaden karatu ga wadanda suka ci jarabawar tantancewar da aka gudanar a dukkan jami’o’in ko kuma kwalejin da ke fadin jahohin kasar nan.

Shugaban Gidauniyar M-TECH, Alhaji Manir Musa Jega, ya bayyana cewa an zabo matasa marasa galihu ne bisa aikin tantancewa da aka yi da nufin samun mabukata na gaskiya ko kuma marasa galihu su iya samun wannan tallafin karatu a kyauta da gidaumiyata ta M-TECH ke bayarwa.

  • Alamomin Cutar Shan Inna Sun Bulla A Kananan Hukumomi 9 Na Jihar Kebbi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar da Aikin Gina Tashar Motoci Ta Zamani A Birnin Kebbi

Kazalika, ya kara da cewa” Gidauniyar na ba su fom din JAMB kyauta da guraben karo ilimi amma ba su da mai taimaka musu da kudi don ci gaba da karatunsu a manyan makarantun da ke fadin jihohin kasar nan. Bisa ga hakan ne gidauniyar M-TECH ke taimakawa don ganin cewa ‘ya’yan marasa galihu ko marayu sun ci gaba da kararunsu a manyan makarantun kasar nan, inji Injiniya Manir Jega”.

Ya ce “mutanen da aka zabo sun fito ne daga kananan hukumomi shida na jihar da suka ci gajiyar tallafin, kuma sun hada da kanana hukumomin Birnin Kebbi da Jega da Bunza da Maiyama da Aliero da Gwandu. Haka kuma an gudanar da wata jarrabawar tantancewa don a zaɓi mafi kyawun su, inji Shugaban gidauniyar M-TECH Injiniya Manir Jega”.

A cewarsa, don karfafa musu gwiwa ne ta hanyar ba su tallafin karatu kuma gidauniyata ta M-TECH ta kafa cibiyar mock ta UTME domin sanar da su dabarun na’ura mai kwakwalwa domin samun nasarar rubuta jarabawar ta kwamfuta. Ya kara da cewa wadanda suka yi nasara za a biya musu kudaden tallafin karatu a cikin manyan makarantun da suka zaba na jahohin kasar Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har ilayau, Injiniya Manir Jega yana kira ga masu hannu da shuni a cikin al’umma da su taimaka wa masu karamin karfi da wadanda suke da kuduri aniyar yin karatu amma iyayensu ba sa raye ko kuma ba su da karfin kudi don daukar nauyin karatun su.

Ya kuma yabawa Gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Dakta Nasir Idris bisa yadda ya zuba jari sosai a fannin ilimi a cikin watanni takwas kacal a kan karagar mulki da ma sauran sassan don ci gaban al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga al’umma a fadin jihar da su ci gaba da baiwa gwamnati mai ci yanzu goyon baya da nufin samun rabon dimokuradiyya tare da yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Next Post

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

1 hour ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

18 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

18 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

19 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

20 hours ago
Next Post
Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.