ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

A kalla yara dari hudu, marayu da masu karamin karfi daga kananan hukumomi shida na jihar Kebbi ne suka samu tallafin karatu daga Gidauniyar M-TECH, ta hanyar ba su fom din JAMB kyauta tare da biyan dukkan kudaden karatu ga wadanda suka ci jarabawar tantancewar da aka gudanar a dukkan jami’o’in ko kuma kwalejin da ke fadin jahohin kasar nan.

Shugaban Gidauniyar M-TECH, Alhaji Manir Musa Jega, ya bayyana cewa an zabo matasa marasa galihu ne bisa aikin tantancewa da aka yi da nufin samun mabukata na gaskiya ko kuma marasa galihu su iya samun wannan tallafin karatu a kyauta da gidaumiyata ta M-TECH ke bayarwa.

  • Alamomin Cutar Shan Inna Sun Bulla A Kananan Hukumomi 9 Na Jihar Kebbi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar da Aikin Gina Tashar Motoci Ta Zamani A Birnin Kebbi

Kazalika, ya kara da cewa” Gidauniyar na ba su fom din JAMB kyauta da guraben karo ilimi amma ba su da mai taimaka musu da kudi don ci gaba da karatunsu a manyan makarantun da ke fadin jihohin kasar nan. Bisa ga hakan ne gidauniyar M-TECH ke taimakawa don ganin cewa ‘ya’yan marasa galihu ko marayu sun ci gaba da kararunsu a manyan makarantun kasar nan, inji Injiniya Manir Jega”.

ADVERTISEMENT

Ya ce “mutanen da aka zabo sun fito ne daga kananan hukumomi shida na jihar da suka ci gajiyar tallafin, kuma sun hada da kanana hukumomin Birnin Kebbi da Jega da Bunza da Maiyama da Aliero da Gwandu. Haka kuma an gudanar da wata jarrabawar tantancewa don a zaɓi mafi kyawun su, inji Shugaban gidauniyar M-TECH Injiniya Manir Jega”.

A cewarsa, don karfafa musu gwiwa ne ta hanyar ba su tallafin karatu kuma gidauniyata ta M-TECH ta kafa cibiyar mock ta UTME domin sanar da su dabarun na’ura mai kwakwalwa domin samun nasarar rubuta jarabawar ta kwamfuta. Ya kara da cewa wadanda suka yi nasara za a biya musu kudaden tallafin karatu a cikin manyan makarantun da suka zaba na jahohin kasar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Har ilayau, Injiniya Manir Jega yana kira ga masu hannu da shuni a cikin al’umma da su taimaka wa masu karamin karfi da wadanda suke da kuduri aniyar yin karatu amma iyayensu ba sa raye ko kuma ba su da karfin kudi don daukar nauyin karatun su.

Ya kuma yabawa Gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Dakta Nasir Idris bisa yadda ya zuba jari sosai a fannin ilimi a cikin watanni takwas kacal a kan karagar mulki da ma sauran sassan don ci gaban al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga al’umma a fadin jihar da su ci gaba da baiwa gwamnati mai ci yanzu goyon baya da nufin samun rabon dimokuradiyya tare da yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.