ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar M-TECH Ta Tallafawa Yara Mabukata 400 Da Tallafin Karatu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

A kalla yara dari hudu, marayu da masu karamin karfi daga kananan hukumomi shida na jihar Kebbi ne suka samu tallafin karatu daga Gidauniyar M-TECH, ta hanyar ba su fom din JAMB kyauta tare da biyan dukkan kudaden karatu ga wadanda suka ci jarabawar tantancewar da aka gudanar a dukkan jami’o’in ko kuma kwalejin da ke fadin jahohin kasar nan.

Shugaban Gidauniyar M-TECH, Alhaji Manir Musa Jega, ya bayyana cewa an zabo matasa marasa galihu ne bisa aikin tantancewa da aka yi da nufin samun mabukata na gaskiya ko kuma marasa galihu su iya samun wannan tallafin karatu a kyauta da gidaumiyata ta M-TECH ke bayarwa.

  • Alamomin Cutar Shan Inna Sun Bulla A Kananan Hukumomi 9 Na Jihar Kebbi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar da Aikin Gina Tashar Motoci Ta Zamani A Birnin Kebbi

Kazalika, ya kara da cewa” Gidauniyar na ba su fom din JAMB kyauta da guraben karo ilimi amma ba su da mai taimaka musu da kudi don ci gaba da karatunsu a manyan makarantun da ke fadin jihohin kasar nan. Bisa ga hakan ne gidauniyar M-TECH ke taimakawa don ganin cewa ‘ya’yan marasa galihu ko marayu sun ci gaba da kararunsu a manyan makarantun kasar nan, inji Injiniya Manir Jega”.

ADVERTISEMENT

Ya ce “mutanen da aka zabo sun fito ne daga kananan hukumomi shida na jihar da suka ci gajiyar tallafin, kuma sun hada da kanana hukumomin Birnin Kebbi da Jega da Bunza da Maiyama da Aliero da Gwandu. Haka kuma an gudanar da wata jarrabawar tantancewa don a zaɓi mafi kyawun su, inji Shugaban gidauniyar M-TECH Injiniya Manir Jega”.

A cewarsa, don karfafa musu gwiwa ne ta hanyar ba su tallafin karatu kuma gidauniyata ta M-TECH ta kafa cibiyar mock ta UTME domin sanar da su dabarun na’ura mai kwakwalwa domin samun nasarar rubuta jarabawar ta kwamfuta. Ya kara da cewa wadanda suka yi nasara za a biya musu kudaden tallafin karatu a cikin manyan makarantun da suka zaba na jahohin kasar Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Har ilayau, Injiniya Manir Jega yana kira ga masu hannu da shuni a cikin al’umma da su taimaka wa masu karamin karfi da wadanda suke da kuduri aniyar yin karatu amma iyayensu ba sa raye ko kuma ba su da karfin kudi don daukar nauyin karatun su.

Ya kuma yabawa Gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Dakta Nasir Idris bisa yadda ya zuba jari sosai a fannin ilimi a cikin watanni takwas kacal a kan karagar mulki da ma sauran sassan don ci gaban al’ummar jihar.

Ya kuma yi kira ga al’umma a fadin jihar da su ci gaba da baiwa gwamnati mai ci yanzu goyon baya da nufin samun rabon dimokuradiyya tare da yin addu’o’in samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar da kasa baki daya.

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

Darussa Daga Rayuwar Shehu Ibrahim Inyass (RA) Wajen Yada Musulunci (II)

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.