• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Sam Nda-Isaiah Ta Miƙa Miliyan 250 Da Gwamna Bago Ya Ba Ɗan Adaidaita Sahun Kano

by Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
Sam

Gidauniyar Sam Nda-Isaiah, ta gabatar da cakin Naira miliyan 250 da Gwamnan Jihar Neja Mohammed Umar Bago, ya bayar domin bai wa direban Adaidaita Sahu, Auwalu Salisu, mazaunin Kano, da ya zama gwarzon matashin kamfanin “LEADERSHIP” na shekarar 2023 bayan tsintar Naira miliyan 15 a babur dinsa kuma mayar ga masu shi.

Babban Editan Jaridar “LEADERSHIP”, Mista Azu Ishiekwene, wanda kuma darakta ne a gidauniyar Sam Nda-Isaiah, shi ya miƙa wa Salisu caki a shalkwatar Kamfanin, bisa shaidawar kawun Salisu, Abba Tukur, da kuma Babban Manajan Gidan Rediyo Arewa, Shehu Bala Kabara.

  • Ba Zan Ce Komai Game Da Rikicin NNPP Ba – Kwankwaso
  • Dole Ne A Tauna Tsakuwa Don Aya Ta Ji Tsoro

Bayan ya miƙa wa Salisu cakin, Ishiekwene ya bayyana godiya ga Gwamna Bago, bisa wannan gudummawar da ya bayar tare da yaba wa wanda ya karɓi cakin na nuna irin wannan abin ban mamaki ta ɗabi’ar gaskiya tare da shawartarsa na ya yi amfani da kuɗaɗen ta hanyar da ta dace.

Cikin jawabinsa a madadin Salisu, Kabara ya jinjina wa kamfanin LEADERSHIP na karramawar da gudunmawar Gwamna Bago, inda ya yi alƙawarin za a yi amfani da kudaden ta hanyar da ya kamata.

Gwamna Bago, ya yi wa Salisu, alƙawarin kyautar Naira miliyan 250 a madadin Shugaba Tinubu da muƙarrabansa da Ƙungiyar Gwamnonin APC, yayin taron shekara-shekara na kamfanin LEADERSHIP.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

Daga baya aka gabatar da Salisu a matsayin gwarzon matashin kamfanin jaridar na 2023 saboda halin gaskiyarsa, gwamnan ya cika alkawarin da ya yi wa Salisu ta hannun Gidauniyar Sam Nda-Isaiah.

Matashin Salisu ya kuma samu tallafin karatu a Jami’ar Baze da ke birnin tarayya Abuja, har zuwa matakin digirin digirgir, daga ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, Peter Obi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa
Labarai

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Next Post
Ingila Ta Dauki Thomas Tuchel A Matsayin Sabon Kocinta

Ingila Ta Dauki Thomas Tuchel A Matsayin Sabon Kocinta

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.