• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ginin Hedkwatar Ecowas: Al’ummar Afrika Ba Za Su Taba Mantawa Da Tallafin Kasar Sin Ba

by CMG Hausa
3 years ago
ECOWAS

Tasiri da taimakon kasar Sin ga nahiyar Afrika kawo yanzu, abubuwa ne da ba za su iya misaltuwa ko bayyanuwa ba, saboda yawansu da kuma karfi da moriyar da suke samarwa. 

A farkon makon nan ne aka aza tubalin ginin hedkwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), a Abuja, babban birnin Nijeriya. Inda ya kasance wani katafaren aiki, kuma babbar nasara ga kungiyar ta ECOWAS, domin a karon farko, muhimman sassanta uku, wato kotun kungiyar da majalisar dokoki da sakatariyarta, za su kasance a dunkule, karkashin inuwa guda maimakon yadda suke a mabambantan wurare.

  • Rukunoni Biyu Na ‘Yan Sama Jannatin Kasar Sin Sun Yi Musayar Aiki A Tashar Binciken Samaniya Ta Sin

Hakika, taimakon kasar Sin na gudanar da wannan aiki tare ma da samar da kudin aiwatar da shi, ya nuna yadda ta damu da ayyukan kungiyar, kuma take fatan ganin nasarori da ci gabansu da ma hadin kansu wajen tunkarar kalubalen dake gabansu, bisa la’akari da yadda kasancewar sassan kungiyar a dunkule, zai rage kudin da ake kashewa tare da kara kaimi kan ayyukan da ake gudanarwa.

Kamar yadda jakadan na Sin a Nijeriya Cui Jianchun ya bayyana, ginin zai taka rawa wajen fadada dangantakar Sin da kasashen yammacin Afrika. A ganinsa, ba kyautata dangantakar Sin da kasashen zai yi ba kadai, har ma tsakanin kasashen kungiyar da kansu a wannan zamani da ake fuskantar dimbin klalubale. Baya ga haka, ya nuna yakinin da Sin ke da shi wajen ganin an samu hadin kai a tsakanin kasashen da ma karfin shawo kan matsalolin dake addabarsu.

Idan muka dubi mai masaukin baki wato Nijeriya da ta bayar da filin ginin, za mu gano cewa, ba kungiyar ECOWAS kadai ce za ta amfana da wannan alheri na kasar Sin ba, domin Nijeriya sai ta fi kowa cin moriya. Kamar yadda hedkwatar kungiyar tarayyar AU da Sin ta gina a Addis Ababa, ya kasance babba, kuma muhimmiyar alama, haka wannan gini ma zai zama wata babbar alama a bangaren gine-gine da kawata birnin Abuja. Haka zalika, tsawon lokacin aikin, zai bunkasa tattalin arzikin yankin da ma birnin, domin zai bude wata kasuwar hada-hada a kowanne bangare na kasuwanci. Har ila yau, zai samar da dimbin guraben ayyukan yi, wanda a ganina, za su rage zaman kashe wando tsakanin matasa da aikata miyagun ayyuka. Bugu da kari, fasahohin da Sin za ta yi amfani da su, zai kara ba Nijeriya gogewa da karin ilimi kan dabaru da fasahohin gine-gine na kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Kamar a ko da yaushe, kasar Sin ta cancanci yabo domin tana kara nuna matsayinta na babbar kasar da ta san ya kamata, kuma aminiya ta kwarai dake da burin ganin ci gaban kawayenta, kuma abun dogaro gare su. Hakika, al’ummar Nijeriya da ma Afrika, ba za su taba mantawa da alherin kasar Sin ba. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.