• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ginin Hedkwatar Ecowas: Al’ummar Afrika Ba Za Su Taba Mantawa Da Tallafin Kasar Sin Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ginin Hedkwatar Ecowas: Al’ummar Afrika Ba Za Su Taba Mantawa Da Tallafin Kasar Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tasiri da taimakon kasar Sin ga nahiyar Afrika kawo yanzu, abubuwa ne da ba za su iya misaltuwa ko bayyanuwa ba, saboda yawansu da kuma karfi da moriyar da suke samarwa. 

A farkon makon nan ne aka aza tubalin ginin hedkwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), a Abuja, babban birnin Nijeriya. Inda ya kasance wani katafaren aiki, kuma babbar nasara ga kungiyar ta ECOWAS, domin a karon farko, muhimman sassanta uku, wato kotun kungiyar da majalisar dokoki da sakatariyarta, za su kasance a dunkule, karkashin inuwa guda maimakon yadda suke a mabambantan wurare.

  • Rukunoni Biyu Na ‘Yan Sama Jannatin Kasar Sin Sun Yi Musayar Aiki A Tashar Binciken Samaniya Ta Sin

Hakika, taimakon kasar Sin na gudanar da wannan aiki tare ma da samar da kudin aiwatar da shi, ya nuna yadda ta damu da ayyukan kungiyar, kuma take fatan ganin nasarori da ci gabansu da ma hadin kansu wajen tunkarar kalubalen dake gabansu, bisa la’akari da yadda kasancewar sassan kungiyar a dunkule, zai rage kudin da ake kashewa tare da kara kaimi kan ayyukan da ake gudanarwa.

Kamar yadda jakadan na Sin a Nijeriya Cui Jianchun ya bayyana, ginin zai taka rawa wajen fadada dangantakar Sin da kasashen yammacin Afrika. A ganinsa, ba kyautata dangantakar Sin da kasashen zai yi ba kadai, har ma tsakanin kasashen kungiyar da kansu a wannan zamani da ake fuskantar dimbin klalubale. Baya ga haka, ya nuna yakinin da Sin ke da shi wajen ganin an samu hadin kai a tsakanin kasashen da ma karfin shawo kan matsalolin dake addabarsu.

Idan muka dubi mai masaukin baki wato Nijeriya da ta bayar da filin ginin, za mu gano cewa, ba kungiyar ECOWAS kadai ce za ta amfana da wannan alheri na kasar Sin ba, domin Nijeriya sai ta fi kowa cin moriya. Kamar yadda hedkwatar kungiyar tarayyar AU da Sin ta gina a Addis Ababa, ya kasance babba, kuma muhimmiyar alama, haka wannan gini ma zai zama wata babbar alama a bangaren gine-gine da kawata birnin Abuja. Haka zalika, tsawon lokacin aikin, zai bunkasa tattalin arzikin yankin da ma birnin, domin zai bude wata kasuwar hada-hada a kowanne bangare na kasuwanci. Har ila yau, zai samar da dimbin guraben ayyukan yi, wanda a ganina, za su rage zaman kashe wando tsakanin matasa da aikata miyagun ayyuka. Bugu da kari, fasahohin da Sin za ta yi amfani da su, zai kara ba Nijeriya gogewa da karin ilimi kan dabaru da fasahohin gine-gine na kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Kamar a ko da yaushe, kasar Sin ta cancanci yabo domin tana kara nuna matsayinta na babbar kasar da ta san ya kamata, kuma aminiya ta kwarai dake da burin ganin ci gaban kawayenta, kuma abun dogaro gare su. Hakika, al’ummar Nijeriya da ma Afrika, ba za su taba mantawa da alherin kasar Sin ba. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Portugal Ko Switzerland, Wa Za Ta Kai Bantenta Bayan Morocco Ta Lallasa Spain?

Next Post

Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

10 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

11 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

12 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

13 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

14 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

16 hours ago
Next Post
Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.