• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ginin Hedkwatar Ecowas: Al’ummar Afrika Ba Za Su Taba Mantawa Da Tallafin Kasar Sin Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ginin Hedkwatar Ecowas: Al’ummar Afrika Ba Za Su Taba Mantawa Da Tallafin Kasar Sin Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tasiri da taimakon kasar Sin ga nahiyar Afrika kawo yanzu, abubuwa ne da ba za su iya misaltuwa ko bayyanuwa ba, saboda yawansu da kuma karfi da moriyar da suke samarwa. 

A farkon makon nan ne aka aza tubalin ginin hedkwatar kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), a Abuja, babban birnin Nijeriya. Inda ya kasance wani katafaren aiki, kuma babbar nasara ga kungiyar ta ECOWAS, domin a karon farko, muhimman sassanta uku, wato kotun kungiyar da majalisar dokoki da sakatariyarta, za su kasance a dunkule, karkashin inuwa guda maimakon yadda suke a mabambantan wurare.

  • Rukunoni Biyu Na ‘Yan Sama Jannatin Kasar Sin Sun Yi Musayar Aiki A Tashar Binciken Samaniya Ta Sin

Hakika, taimakon kasar Sin na gudanar da wannan aiki tare ma da samar da kudin aiwatar da shi, ya nuna yadda ta damu da ayyukan kungiyar, kuma take fatan ganin nasarori da ci gabansu da ma hadin kansu wajen tunkarar kalubalen dake gabansu, bisa la’akari da yadda kasancewar sassan kungiyar a dunkule, zai rage kudin da ake kashewa tare da kara kaimi kan ayyukan da ake gudanarwa.

Kamar yadda jakadan na Sin a Nijeriya Cui Jianchun ya bayyana, ginin zai taka rawa wajen fadada dangantakar Sin da kasashen yammacin Afrika. A ganinsa, ba kyautata dangantakar Sin da kasashen zai yi ba kadai, har ma tsakanin kasashen kungiyar da kansu a wannan zamani da ake fuskantar dimbin klalubale. Baya ga haka, ya nuna yakinin da Sin ke da shi wajen ganin an samu hadin kai a tsakanin kasashen da ma karfin shawo kan matsalolin dake addabarsu.

Idan muka dubi mai masaukin baki wato Nijeriya da ta bayar da filin ginin, za mu gano cewa, ba kungiyar ECOWAS kadai ce za ta amfana da wannan alheri na kasar Sin ba, domin Nijeriya sai ta fi kowa cin moriya. Kamar yadda hedkwatar kungiyar tarayyar AU da Sin ta gina a Addis Ababa, ya kasance babba, kuma muhimmiyar alama, haka wannan gini ma zai zama wata babbar alama a bangaren gine-gine da kawata birnin Abuja. Haka zalika, tsawon lokacin aikin, zai bunkasa tattalin arzikin yankin da ma birnin, domin zai bude wata kasuwar hada-hada a kowanne bangare na kasuwanci. Har ila yau, zai samar da dimbin guraben ayyukan yi, wanda a ganina, za su rage zaman kashe wando tsakanin matasa da aikata miyagun ayyuka. Bugu da kari, fasahohin da Sin za ta yi amfani da su, zai kara ba Nijeriya gogewa da karin ilimi kan dabaru da fasahohin gine-gine na kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Kamar a ko da yaushe, kasar Sin ta cancanci yabo domin tana kara nuna matsayinta na babbar kasar da ta san ya kamata, kuma aminiya ta kwarai dake da burin ganin ci gaban kawayenta, kuma abun dogaro gare su. Hakika, al’ummar Nijeriya da ma Afrika, ba za su taba mantawa da alherin kasar Sin ba. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Portugal Ko Switzerland, Wa Za Ta Kai Bantenta Bayan Morocco Ta Lallasa Spain?

Next Post

Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

Related

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

11 minutes ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

1 hour ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

3 hours ago
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

21 hours ago
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi
Daga Birnin Sin

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

22 hours ago
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba
Daga Birnin Sin

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

22 hours ago
Next Post
Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

Nuna Bambanci Ga Sin Da Kayyade Hadin Gwiwa Tare Da Sin Ba Su Dace Da Moriyar Kowane Bangaren Duniya Ba

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.