• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar-kasar Turkiyya Da Siriya Ta Jefa Duniya Cikin Alhini

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Ya Kamata Amurka Ta Dage Takunkumin Da Ta Kakabawa Syria Nan Take
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanayin girgizar-kasa mai karfin gaske da ta auku a kasashen Turkiyya da Siriya ya jefa duniya cikin alhini sakamakon dubban mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, ya zuwa ranar laraba an tabbatar da mutuwar mutum 7,000.

Rabon a ga girgizar-kasa mai barna irin wannan a duniya tun a shekarar 1999 lokacin da kimanin mutum dubu 17 suka rasa rayukansu.

  • Girgizar Kasa: Adadin Wadanda Suka Mutu A Turkiyya Da Siriya Sun Haura 23,000

Bayan aukuwar lamarin dai, masu aikin ceto sun dukufa fafutikar ganin ko za a samo wasu da ransu a karkashin baraguzan gine-ginen da suka rufta a wasu yankunan kasashen Turkiyya da Siriya.

Sai dai ruwan sama mai karfi da dusar kankara wadda ke zuba sun rika kawo cikas ga aikin a kudu maso gabashin Turkiyya.
Shafin Hausa na BBC ya ruwaito Hukumar Lafiya ta Duniya na gargadin cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka rasa ransu a lamarin zai yi matukar karuwa.

Mutane da dama a yankunan da lamarin ya faru na jin tsoron komawa cikin gine-gine da suka rage.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

Masu nazari kan motsin kasa sun ce girgizar ita ce mafi girma da aka taba samu a Turkiyya.

Al’ummar yankin sun ce an kwashe minti biyu kasa na jijjiga kafin lamarin ya dakata.
Alkaluma daga Turkiyya da Siriya na nuna cewa kawo yanzu mutum fiye da dubu biyar ne suka mutu sannan fiye da dubu 15 suka jikkata sakamakon ibtila’in girgizar kasar.

Shugabanni kasashen duniya sun yi alkawarin aikewa da tawagar ma’aikata da kayan aikin ceto ya zuwa Turkiyya don agazawa.

Rahotanni na cewa an kara samun girgizar kasa karo na biyu cikin kwana guda a kudu-maso-gabashin Turkiyya.

Hukumar lura da yanayin kasa ta Amurka ta ce karfin girgizar kasar ya kai 7.5 a kan ma’auni.

Lamarin ya faru ne a gundumar Elbistan na lardin Kahramanmaras.
Wani jami’in Hukumar Lura da Bala’o’i na Turkiyya ya tabbatar da cewa “wannan wata sabuwar girgizar kasa ce ba ragowar wadda ta faru ne a farko ba.”

Wani faifan bidiyo ya nuna yadda mutane ke gudu cikin rudewa a lokacin da girgizar ta biyu ta faru.

An ga mutanen suna ihu, suna gudu a kan tituna a lokacin da kura ke lafawa bayan gine-gine sun rufta.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta afka wa yankin Gaziantep da ke kudancin Turkiyya a tsakiyar daren Litinin.

Kuma an jiyo ruguginta har a yankin Gaza. An kuma samu rushewar gidaje a Lebanon.
Turkiyya dai ta ayyana dokar ta baci tare da kira ga mutane su dakatar da amfani da wayoyinsu, saboda masu aikin agaji su samu damar kai wa ga wadanda suka makale a cikin baraguzai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Goyon Bayan Kamfanoninta Su Kiyaye Moriyarsu Bisa Doka

Next Post

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

32 minutes ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

2 hours ago
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

4 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

6 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

8 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

11 hours ago
Next Post
’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.