ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar-kasar Turkiyya Da Siriya Ta Jefa Duniya Cikin Alhini

by Bello Hamza
3 years ago
Girgizar-kasar Turkiyya da Siriya

Yanayin girgizar-kasa mai karfin gaske da ta auku a kasashen Turkiyya da Siriya ya jefa duniya cikin alhini sakamakon dubban mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, ya zuwa ranar laraba an tabbatar da mutuwar mutum 7,000.

Rabon a ga girgizar-kasa mai barna irin wannan a duniya tun a shekarar 1999 lokacin da kimanin mutum dubu 17 suka rasa rayukansu.

  • Girgizar Kasa: Adadin Wadanda Suka Mutu A Turkiyya Da Siriya Sun Haura 23,000

Bayan aukuwar lamarin dai, masu aikin ceto sun dukufa fafutikar ganin ko za a samo wasu da ransu a karkashin baraguzan gine-ginen da suka rufta a wasu yankunan kasashen Turkiyya da Siriya.

ADVERTISEMENT

Sai dai ruwan sama mai karfi da dusar kankara wadda ke zuba sun rika kawo cikas ga aikin a kudu maso gabashin Turkiyya.
Shafin Hausa na BBC ya ruwaito Hukumar Lafiya ta Duniya na gargadin cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka rasa ransu a lamarin zai yi matukar karuwa.

Mutane da dama a yankunan da lamarin ya faru na jin tsoron komawa cikin gine-gine da suka rage.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Masu nazari kan motsin kasa sun ce girgizar ita ce mafi girma da aka taba samu a Turkiyya.

Al’ummar yankin sun ce an kwashe minti biyu kasa na jijjiga kafin lamarin ya dakata.
Alkaluma daga Turkiyya da Siriya na nuna cewa kawo yanzu mutum fiye da dubu biyar ne suka mutu sannan fiye da dubu 15 suka jikkata sakamakon ibtila’in girgizar kasar.

Shugabanni kasashen duniya sun yi alkawarin aikewa da tawagar ma’aikata da kayan aikin ceto ya zuwa Turkiyya don agazawa.

Rahotanni na cewa an kara samun girgizar kasa karo na biyu cikin kwana guda a kudu-maso-gabashin Turkiyya.

Hukumar lura da yanayin kasa ta Amurka ta ce karfin girgizar kasar ya kai 7.5 a kan ma’auni.

Lamarin ya faru ne a gundumar Elbistan na lardin Kahramanmaras.
Wani jami’in Hukumar Lura da Bala’o’i na Turkiyya ya tabbatar da cewa “wannan wata sabuwar girgizar kasa ce ba ragowar wadda ta faru ne a farko ba.”

Wani faifan bidiyo ya nuna yadda mutane ke gudu cikin rudewa a lokacin da girgizar ta biyu ta faru.

An ga mutanen suna ihu, suna gudu a kan tituna a lokacin da kura ke lafawa bayan gine-gine sun rufta.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta afka wa yankin Gaziantep da ke kudancin Turkiyya a tsakiyar daren Litinin.

Kuma an jiyo ruguginta har a yankin Gaza. An kuma samu rushewar gidaje a Lebanon.
Turkiyya dai ta ayyana dokar ta baci tare da kira ga mutane su dakatar da amfani da wayoyinsu, saboda masu aikin agaji su samu damar kai wa ga wadanda suka makale a cikin baraguzai.

Girgizar-kasar Turkiyya da Siriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.