ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar-kasar Turkiyya Da Siriya Ta Jefa Duniya Cikin Alhini

by Bello Hamza
4 years ago
Girgizar-kasar Turkiyya da Siriya

Yanayin girgizar-kasa mai karfin gaske da ta auku a kasashen Turkiyya da Siriya ya jefa duniya cikin alhini sakamakon dubban mutanen da suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka jikkata, ya zuwa ranar laraba an tabbatar da mutuwar mutum 7,000.

Rabon a ga girgizar-kasa mai barna irin wannan a duniya tun a shekarar 1999 lokacin da kimanin mutum dubu 17 suka rasa rayukansu.

  • Girgizar Kasa: Adadin Wadanda Suka Mutu A Turkiyya Da Siriya Sun Haura 23,000

Bayan aukuwar lamarin dai, masu aikin ceto sun dukufa fafutikar ganin ko za a samo wasu da ransu a karkashin baraguzan gine-ginen da suka rufta a wasu yankunan kasashen Turkiyya da Siriya.

ADVERTISEMENT

Sai dai ruwan sama mai karfi da dusar kankara wadda ke zuba sun rika kawo cikas ga aikin a kudu maso gabashin Turkiyya.
Shafin Hausa na BBC ya ruwaito Hukumar Lafiya ta Duniya na gargadin cewa akwai yiwuwar yawan wadanda suka rasa ransu a lamarin zai yi matukar karuwa.

Mutane da dama a yankunan da lamarin ya faru na jin tsoron komawa cikin gine-gine da suka rage.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Masu nazari kan motsin kasa sun ce girgizar ita ce mafi girma da aka taba samu a Turkiyya.

Al’ummar yankin sun ce an kwashe minti biyu kasa na jijjiga kafin lamarin ya dakata.
Alkaluma daga Turkiyya da Siriya na nuna cewa kawo yanzu mutum fiye da dubu biyar ne suka mutu sannan fiye da dubu 15 suka jikkata sakamakon ibtila’in girgizar kasar.

Shugabanni kasashen duniya sun yi alkawarin aikewa da tawagar ma’aikata da kayan aikin ceto ya zuwa Turkiyya don agazawa.

Rahotanni na cewa an kara samun girgizar kasa karo na biyu cikin kwana guda a kudu-maso-gabashin Turkiyya.

Hukumar lura da yanayin kasa ta Amurka ta ce karfin girgizar kasar ya kai 7.5 a kan ma’auni.

Lamarin ya faru ne a gundumar Elbistan na lardin Kahramanmaras.
Wani jami’in Hukumar Lura da Bala’o’i na Turkiyya ya tabbatar da cewa “wannan wata sabuwar girgizar kasa ce ba ragowar wadda ta faru ne a farko ba.”

Wani faifan bidiyo ya nuna yadda mutane ke gudu cikin rudewa a lokacin da girgizar ta biyu ta faru.

An ga mutanen suna ihu, suna gudu a kan tituna a lokacin da kura ke lafawa bayan gine-gine sun rufta.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta afka wa yankin Gaziantep da ke kudancin Turkiyya a tsakiyar daren Litinin.

Kuma an jiyo ruguginta har a yankin Gaza. An kuma samu rushewar gidaje a Lebanon.
Turkiyya dai ta ayyana dokar ta baci tare da kira ga mutane su dakatar da amfani da wayoyinsu, saboda masu aikin agaji su samu damar kai wa ga wadanda suka makale a cikin baraguzai.

Girgizar-kasar Turkiyya da Siriya
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-15 Na Kasar Sin Sun Kammala Tattakin Farko A Wajen Tashar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.