• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Yara Biyu A Madina Kwatas Da Ke Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gobara Ta Hallaka Yara Biyu A Madina Kwatas Da Ke Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar unguwar Madina Kwatas sun tashi da mummunar ibtila’in gobara wacce ta yi sanadin rasa yara kanana biyu – Zainab Bashir Muhammad (Hibba) mai shekara 7 da kuma Ummu Salma Bashir (Afnan) mai shekara 5 a duniya.

Gobarar wacce ta tashi a makwabtar wakilinmu da ke unguwar Madina quarters a kusa da makarantar Barden Gabas da ke yankin Turwun, ya rahoto cewa, gobarar ta tashi ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Dokar Masana’antar Fetur (PIB): Yadda Aka Yi Wa Kudin Man Fetur Kofar-raggo A Nijeriya

Abun da ya faru kuwa shi ne, mahaifiyar yaran ta fita unguwa inda ta bar yaranta biyu a cikin daki bayan ta kulle dakin tare da kofar gida.

“Lokacin da muka ji wutar ta tashi mun nufi gidan ni da makwabtana, mun yi duk kokarin balle kofar gidan amma hakan ya cutura sai da aka nemo guduma aka balle. Ana wannan gabar, mun yi kokarin haurawa gidan ta sama, inda muka tarar da wutar ci karfin dakin da yaran suke.

“Bayan shiganmu cikin gidan, mun yi kokarin balle kofar dakin amma hakan ba ta yiwu ba. Wuta ce sosai da hayaki mai illa matuka,” In ji wakilinmu da lamarin ya wakana a kan idonsa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Kazalika, Usman Abdullahi (Dan Usmanu) ya shaida cewar, “Allah dai ya aiko da tsautsayi amma ba dabi’ar matar ba ne kulle yara a gida. Wani lokacin in za ta fita ta na kawo yaranta gidana saboda gidan na kusa da kofar gidana.

“Mijinta mai suna Bash baya nan a lokacin da wutar ta tashi. Har yanzu dai ba mu gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar ba.

“Sai dai abun takaici duk da kokarin namu mun kasa ceto yaran. Allah sa masu ceto ne.”

“Babu abun da aka cire a cikin gidan komai ya kone kurmus. Dabbobi ne kawai mutane suka iya cirosu ta saman garu, amma bayan tumakin gidan komai ya kone kurmus.”

Wakilinmu ya kuma shaida mana cewar, jami’an kashe gobara na jihar sun yi kokarin zuwa a kan lokaci wanda sun bada gagarumin gudunmawa wajen kashe wutar.

Sai dai lamarin ya tayar wa al’ummar unguwar hankali matuka.

Tuni aka yi jana’izar yaran kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Shirya Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Next Post

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Gobara
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post
Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.