• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Yara Biyu A Madina Kwatas Da Ke Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gobara Ta Hallaka Yara Biyu A Madina Kwatas Da Ke Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar unguwar Madina Kwatas sun tashi da mummunar ibtila’in gobara wacce ta yi sanadin rasa yara kanana biyu – Zainab Bashir Muhammad (Hibba) mai shekara 7 da kuma Ummu Salma Bashir (Afnan) mai shekara 5 a duniya.

Gobarar wacce ta tashi a makwabtar wakilinmu da ke unguwar Madina quarters a kusa da makarantar Barden Gabas da ke yankin Turwun, ya rahoto cewa, gobarar ta tashi ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Dokar Masana’antar Fetur (PIB): Yadda Aka Yi Wa Kudin Man Fetur Kofar-raggo A Nijeriya

Abun da ya faru kuwa shi ne, mahaifiyar yaran ta fita unguwa inda ta bar yaranta biyu a cikin daki bayan ta kulle dakin tare da kofar gida.

“Lokacin da muka ji wutar ta tashi mun nufi gidan ni da makwabtana, mun yi duk kokarin balle kofar gidan amma hakan ya cutura sai da aka nemo guduma aka balle. Ana wannan gabar, mun yi kokarin haurawa gidan ta sama, inda muka tarar da wutar ci karfin dakin da yaran suke.

“Bayan shiganmu cikin gidan, mun yi kokarin balle kofar dakin amma hakan ba ta yiwu ba. Wuta ce sosai da hayaki mai illa matuka,” In ji wakilinmu da lamarin ya wakana a kan idonsa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

Kazalika, Usman Abdullahi (Dan Usmanu) ya shaida cewar, “Allah dai ya aiko da tsautsayi amma ba dabi’ar matar ba ne kulle yara a gida. Wani lokacin in za ta fita ta na kawo yaranta gidana saboda gidan na kusa da kofar gidana.

“Mijinta mai suna Bash baya nan a lokacin da wutar ta tashi. Har yanzu dai ba mu gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar ba.

“Sai dai abun takaici duk da kokarin namu mun kasa ceto yaran. Allah sa masu ceto ne.”

“Babu abun da aka cire a cikin gidan komai ya kone kurmus. Dabbobi ne kawai mutane suka iya cirosu ta saman garu, amma bayan tumakin gidan komai ya kone kurmus.”

Wakilinmu ya kuma shaida mana cewar, jami’an kashe gobara na jihar sun yi kokarin zuwa a kan lokaci wanda sun bada gagarumin gudunmawa wajen kashe wutar.

Sai dai lamarin ya tayar wa al’ummar unguwar hankali matuka.

Tuni aka yi jana’izar yaran kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Shirya Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2

Next Post

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Related

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

8 minutes ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

25 minutes ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

1 hour ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

4 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

12 hours ago
Next Post
Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.