Akalla wasu ‘yan gudun hijira uku ne suka rasu sannan sama da gidaje 1000 suka kone bayan da gobara ta tashi a sansanin ‘yan gudun hijira na Muna Alamdari da ke Maiduguri a Jihar Borno.
Gobarar ta tashi ne da misalin karfe 6 na safiyar Laraba kuma ta dauki sama da awa daya kafin jami’an kashe gobara su shawo kan ta.
- Mun Yarda Mu Hada Kai Da Atiku In Zai Marawa Kwankwaso Baya A 2027 – NNPP
- Gwamnan Jigawa Ya Gabatar Da Kasafin Naira Biliyan N298.14bn Na Shekarar 2024
Babban Darakta Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar, Dokta Barkindo Muhammad Sa’idu ne, ya bayyana hakan a Maiduguri ga manema labarai.
Ya ce jami’an sa-kai na CJTF, da jami’an tsaro da ‘yan gudun hijira, sun taimaka wajen kashe gobarar.
An samu asarar dukiya a sanadin tashin gobarar.
Tuni dai gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum ya kafa kwamiti don gudanar da binciken musababbin tashin gobarar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp