• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
BudgetIT

Jihar Gombe ta samu nasara a kididdigar kasafin kudi na 2023 wadda BudgetIT ta wallafa, wacce cibiya ce da ta shahara wajen bin diddigin manufofin kudi a Nijeriya.

Jihar ta zo matsayi na 6 daga cikin jihohi 36, inda ta samu maki 74 bisa 100.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Rahoton ya yaba da irin nasarorin da Jihar Gombe ta samu a fannoni daban-daban da suka hada da nuna gaskiya a harkokin kasafi da kashe-kashen kudi, da nuna aminci da sahihanci a rahoton gudanar da kasafin kudi ta shafin yanar gizon jihar.

Wani babban abin lura ma shine tsarin kasafin kudin jihar na matsakaicin zango (MTEF), wanda aka bayyana shi a matsayin cikakke kuma mai kyakkywan tsari.

Rahoton ya tabbatar da cewa kasafin kudin Jihar Gombe da aka amince da shi ya cika sharuda da dama, yayin da harkokin kashe-kashen kudi na yanar gizon jihar ya kasance a saukake ga mai bukatar bincike da nazari.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Bugu da kari, Jihar Gombe ta kasance ta 7 a Nijeriya, yayin da a yankin Arewa maso gabas kuwa ta yi fintinkau a fannin gudanar da ayyuka cikin gaskiya da rikon amana, matsayin da ta samu daga cibiyar kula da harkokin kudi ta ƙasa (CETIW).

Farfesa kuma mai bincike da nazari a fannoni daban-daban, wanda kuma shi ne babban daraktan bincike da tattara bayanai a gidan gwamnati, Dr. Mu’azu Shehu ya bayyana cewa, bisa la’akari da yadda yake sanya ido sosai kan ayyukan gwamnati da kuma kimanta ci gaban kasa, Jihar Gombe ta yi fintinkau a fannin tafiyar da harkokin kudi cikin gaskiya da adalci da ɗorewar ayyuka na gari.

Ya yi nuni da cewa, shugabancin Gwamna Inuwa Yahaya ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da shugabanci nagari da kuma tabbatar da gaskiya, tare da sanya Jihar Gombe a matsayin Jihar da samu shugabacin mai cike da riƙon amana ba tare da nuna wariya ba.

“Gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya tana ci gaba da jaddada kudirinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana a kasafin kudi, wanda hakan ya sa Jihar Gombe ta samu karramawa a matakin kasa da na kasa da kasa. Musamman ma, a kwanan nan jihar ta samu lambar yabo na Bankin Duniya a Fannin tabbatar da gaskiya, adalci da dorewarsu wato (SFTAS) a fannoni dandan daban, hakan wata shaida ce dake nuna irin jajircewar gwamnatin Inuwa wajen kulawa da dukiyar talakawa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.