• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihar Gombe ta samu nasara a kididdigar kasafin kudi na 2023 wadda BudgetIT ta wallafa, wacce cibiya ce da ta shahara wajen bin diddigin manufofin kudi a Nijeriya.

Jihar ta zo matsayi na 6 daga cikin jihohi 36, inda ta samu maki 74 bisa 100.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Rahoton ya yaba da irin nasarorin da Jihar Gombe ta samu a fannoni daban-daban da suka hada da nuna gaskiya a harkokin kasafi da kashe-kashen kudi, da nuna aminci da sahihanci a rahoton gudanar da kasafin kudi ta shafin yanar gizon jihar.

Wani babban abin lura ma shine tsarin kasafin kudin jihar na matsakaicin zango (MTEF), wanda aka bayyana shi a matsayin cikakke kuma mai kyakkywan tsari.

Rahoton ya tabbatar da cewa kasafin kudin Jihar Gombe da aka amince da shi ya cika sharuda da dama, yayin da harkokin kashe-kashen kudi na yanar gizon jihar ya kasance a saukake ga mai bukatar bincike da nazari.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Bugu da kari, Jihar Gombe ta kasance ta 7 a Nijeriya, yayin da a yankin Arewa maso gabas kuwa ta yi fintinkau a fannin gudanar da ayyuka cikin gaskiya da rikon amana, matsayin da ta samu daga cibiyar kula da harkokin kudi ta ƙasa (CETIW).

Farfesa kuma mai bincike da nazari a fannoni daban-daban, wanda kuma shi ne babban daraktan bincike da tattara bayanai a gidan gwamnati, Dr. Mu’azu Shehu ya bayyana cewa, bisa la’akari da yadda yake sanya ido sosai kan ayyukan gwamnati da kuma kimanta ci gaban kasa, Jihar Gombe ta yi fintinkau a fannin tafiyar da harkokin kudi cikin gaskiya da adalci da ɗorewar ayyuka na gari.

Ya yi nuni da cewa, shugabancin Gwamna Inuwa Yahaya ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da shugabanci nagari da kuma tabbatar da gaskiya, tare da sanya Jihar Gombe a matsayin Jihar da samu shugabacin mai cike da riƙon amana ba tare da nuna wariya ba.

“Gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya tana ci gaba da jaddada kudirinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana a kasafin kudi, wanda hakan ya sa Jihar Gombe ta samu karramawa a matakin kasa da na kasa da kasa. Musamman ma, a kwanan nan jihar ta samu lambar yabo na Bankin Duniya a Fannin tabbatar da gaskiya, adalci da dorewarsu wato (SFTAS) a fannoni dandan daban, hakan wata shaida ce dake nuna irin jajircewar gwamnatin Inuwa wajen kulawa da dukiyar talakawa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Tsibbu Da Kan Mutum A Jihar Ondo 

Next Post

An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

6 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

7 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.