ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al’umma

by Sulaiman
3 years ago
BudgetIT

Jihar Gombe ta samu nasara a kididdigar kasafin kudi na 2023 wadda BudgetIT ta wallafa, wacce cibiya ce da ta shahara wajen bin diddigin manufofin kudi a Nijeriya.

Jihar ta zo matsayi na 6 daga cikin jihohi 36, inda ta samu maki 74 bisa 100.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Rahoton ya yaba da irin nasarorin da Jihar Gombe ta samu a fannoni daban-daban da suka hada da nuna gaskiya a harkokin kasafi da kashe-kashen kudi, da nuna aminci da sahihanci a rahoton gudanar da kasafin kudi ta shafin yanar gizon jihar.

ADVERTISEMENT

Wani babban abin lura ma shine tsarin kasafin kudin jihar na matsakaicin zango (MTEF), wanda aka bayyana shi a matsayin cikakke kuma mai kyakkywan tsari.

Rahoton ya tabbatar da cewa kasafin kudin Jihar Gombe da aka amince da shi ya cika sharuda da dama, yayin da harkokin kashe-kashen kudi na yanar gizon jihar ya kasance a saukake ga mai bukatar bincike da nazari.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Bugu da kari, Jihar Gombe ta kasance ta 7 a Nijeriya, yayin da a yankin Arewa maso gabas kuwa ta yi fintinkau a fannin gudanar da ayyuka cikin gaskiya da rikon amana, matsayin da ta samu daga cibiyar kula da harkokin kudi ta ƙasa (CETIW).

Farfesa kuma mai bincike da nazari a fannoni daban-daban, wanda kuma shi ne babban daraktan bincike da tattara bayanai a gidan gwamnati, Dr. Mu’azu Shehu ya bayyana cewa, bisa la’akari da yadda yake sanya ido sosai kan ayyukan gwamnati da kuma kimanta ci gaban kasa, Jihar Gombe ta yi fintinkau a fannin tafiyar da harkokin kudi cikin gaskiya da adalci da ɗorewar ayyuka na gari.

Ya yi nuni da cewa, shugabancin Gwamna Inuwa Yahaya ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da shugabanci nagari da kuma tabbatar da gaskiya, tare da sanya Jihar Gombe a matsayin Jihar da samu shugabacin mai cike da riƙon amana ba tare da nuna wariya ba.

“Gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya tana ci gaba da jaddada kudirinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana a kasafin kudi, wanda hakan ya sa Jihar Gombe ta samu karramawa a matakin kasa da na kasa da kasa. Musamman ma, a kwanan nan jihar ta samu lambar yabo na Bankin Duniya a Fannin tabbatar da gaskiya, adalci da dorewarsu wato (SFTAS) a fannoni dandan daban, hakan wata shaida ce dake nuna irin jajircewar gwamnatin Inuwa wajen kulawa da dukiyar talakawa.”

BudgetIT
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • Sulaiman
    Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
BudgetIT
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
BudgetIT
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
BudgetIT

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
BudgetIT

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.