• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudummawar Sin Ga Aikin Samar Da Duniya Mai Tsafta Da Kyan Gani

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Gudummawar Sin Ga Aikin Samar Da Duniya Mai Tsafta Da Kyan Gani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Burin dukkanin bil adama ne samun kyakkyawar rayuwa, da muhalli mai tsafta da kyan gani, mai ruwa garai-garai, da tsaunuka masu kayatarwa, da muhallin halittu mai ni’ima, wato dai muhallin da dan adam da sauran halittun dake kewaye da shi ke zaune cikin lumana da juna. 

Yayin da nake kara samun zarafin ziyartar sassan kasar Sin daban daban, ina kara ganin wasu manufofi da mahukuntan kasar ke aiwatarwa, ta fuskar daidaita zaman rayuwar bil adama da sassan halittu, da muhallin dake kewaye da shi, tare da hada gwiwa da sauran kasashen duniya wajen gina duniya mai tsafta da kyan gani.

  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Yi Fatali Da Kudirin Sake Fasalin Dokar Haraji

Salon zamanantarwa na Sin na kunshe da manufar zaman jituwa tsakanin mutane da halittun dake kewaye da su. A halin da ake ciki, kasar Sin na ci gaba da samun manyan nasarori a fagen bunkasa kasa ba tare da gurbata muhalli ba. A daya hannun kasar Sin na ta kara raba dabarunta na kyautata muhalli tare da sauran sassan kasa da kasa.

Karkashin hakan, kasar Sin na aiwatar da manufofi da suka hada da kafa ginshikin zamanantarwa irin ta Sin, da hada gwiwa da sauran sassa wajen ingiza burin samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma goyon bayan jagorancin inganta muhalli a matakin kasa da kasa, ta yadda za a gudu tare a tsira tare

Kawo yanzu, Sin ta sanya hannu kan takardun fahimtar juna da dama, masu nasaba da hadin gwiwar kyautata yanayi, tare da kasashe masu saurin bunkasa da kasashe masu tasowa, ta kuma fara aiwatar da tarin ayyukan dakile mummunan tasirin yanayi, da samar da juriyar tasirin hakan. Har ila yau, Sin ta dauki nauyin gudanar da tarukan karawa juna sani sama da 300 a fannin dakile sauyin yanayi.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Alal hakika, Sin ta yi imanin cewa daukacin bil adama na da makoma ce ta bai daya, don haka take dagewa tukuru, wajen ba da gudummawar gina duniya mai tsafta da kayatarwa ga kowa.

Shaidun zahiri sun tabbatar da kwazon Sin a fannin ingiza zamanantarwa ta Sin a fannin zaman jituwa tsakanin mutum da halittun da yake rayuwa tare da su, tana kuma himma wajen yaukaka musaya, da hadin gwiwa da sauran sassa a ayyukan kare muhallin halittu, ta yadda daukacin bil adama zai more kyakkyawar rayuwa, da makoma mai haske ta bai daya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ta Ja Kunnen Matafiya Ƙasashe Bakwai A Afrika

Next Post

Sin Ta Kara Sassa 28 Na Amurka Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Shigar Musu Da Kayayyaki 

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

16 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

17 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

18 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

19 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

20 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

21 hours ago
Next Post
Sin Ta Kara Sassa 28 Na Amurka Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Shigar Musu Da Kayayyaki 

Sin Ta Kara Sassa 28 Na Amurka Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Shigar Musu Da Kayayyaki 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.