• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

byIdris Aliyu Daudawa
1 year ago
Gudunmawa

Ilimi na matukar bayar da gudunmawa wajen ci gaban al’umma, musamman ma idan ya kasance akwai masu ilimi da dama a cikin al’ummar. Ga dai wasu daga cikin gudunmawar da ilimin ke bayarwa kamar haka:

1. Samar Da Hanyoyin Ayyukan Yi
Samun aikin yi, ba karamin lamari ba ne; musamman a irin halin da ake ciki yanzu na matsalar tattalin arziki da tsadar rayuwa.
Ko shakka babu, yanzu haka ana cikin wani irin yanayi ne na gwagwagwa da daruruwan wadanda suka kammala makaranta, ba tare da samun aiki yi ba.
Haka zalika, abin la’akari a nan shi ne; idan ilimin da ake da shi ba wani mai zurfi ba ne, za a iya samun mutane da yawa da suke neman aiki.
Amma, idan kuma ilimin mai zurfi ne, wato kamar makarantar gaba da Sakandire, ilimin da aka fi so da yadda aka fara yin sa, akwai yiwuwar samun aiki; ba sai an wani bata lokaci ba, sannan za a iya samun albashi mai tsoka.
Don haka, idan har kana bukatar kasancewa cikin wadanda za a rika yin wawarsu, sakamakon tsayawa da suka yi suka jajirce wajen yin karatu, wajibi ne kai ma ka mayar da hankali a makaranta har sai ka cimma naka burin na karatu.

2. Samun Kudade Ta Hanyoyi Daban-daban
Wadanda suka tsaya suka yi karatu a makarantun gaba da Sakandire tare da samun kwarewa a fannoni daban-daban, na daya daga cikin wadanda za su samu aikin yi; ba tare da shan wuya ba, domin kuwa har daga kasashen waje za a rika rubibin su.
Don haka, A yi kokari wajen yin wannan karatu yadda ya dace tare da samar da lokaci; domin samun irin ilimin da ake bukata, irin haka ne ke sa wa a samu rayuwa mai inganci; wadda kowa da kowa zai yi sha’awar kasancewa cikinta.
Takardunka ko satifiket daban-daban da ka samu, su ne za su yi bayanin ko kai wane ne, su ne kuma za su ja hankalin masu daukar ka aiki. Saboda haka, lallai a yi karatu tukuru a makaranta; duk tsawon lokaci ko shekarun da za a dauka kafin a gama.
Kazalika, ta hanyar duba wannan satifiket ne, masu daukar aiki ke iya gane, wadanda suka mayar da hankali a karatunsu, suka kuma san abin da suke yi.

3. Samar Da Ilimin Da Za A Yi Maganin Wasu Matsaloli
Daya daga cikin muhimmancin ilimi shi ne, koya mana yadda za mu samu ilimi tare da yin amfani da shi wajen yin tunani, domin daukar matakin da zai taimaka mana a rayuwarmu.
Kamar yadda aka sani ne, bayan yara sun kammala karatunsu sun samu aiki yi, nauyi tare da matsaloli na hawa kansu ta fuskoki da dama, da farko dai yadda za su biya bashin da suka karba a lokacin sa suna makaranta da yadda za su mallaki gida ko mahalli da kokarin sayen mota da kuma biya wa iyali nasu bukatun da dai sauran makamantansu.
Koda-yake, mutane da dama na shafe shekara da shekaru wajen gwagwarmayar neman wannan ilimi, duk da hakan ya dace a ce suna iya daukar mataki dangane da wasu al’amura nasu. Amma, abin bai tsaya kadai a nan ba, domin kuwa akwai bukatar har sai idan har sun kai ga samun mafita kan matakan da suka dauka; domin samun ingantacciyar rayuwa da kuma ci gaba.

4. Bunkasa Tattalin Arziki
Mafi yawan lokuta, mutanen da suka samu ilimi mai zurfi da nagarta, sun fi samun ayyukan da ake biyan albashi mai tsoka, yadda mutum ya mallaki takardu ko satifiket na ilimi mai zurfi da muhimmanci, irin hakan ne ke bayar da damar samun aiki mai nagarta, inda za a rika ba da albashi mai matukar tsoka.
Har ila yau, ilimi na taimaka wa kasashe wajen samun bunkasa da ci gaban tattalin arziki, sakamakon ilimin da Allah yah ore musu tare da sanin hanyoyin da za su sarrafa shi da kuma yin amfani da shi yadda ya kamata, musamman wajen bunkasa rayuwar al’ummarsu.

LABARAI MASU NASABA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version