ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Gudunmawa

Ilimi na matukar bayar da gudunmawa wajen ci gaban al’umma, musamman ma idan ya kasance akwai masu ilimi da dama a cikin al’ummar. Ga dai wasu daga cikin gudunmawar da ilimin ke bayarwa kamar haka:

1. Samar Da Hanyoyin Ayyukan Yi
Samun aikin yi, ba karamin lamari ba ne; musamman a irin halin da ake ciki yanzu na matsalar tattalin arziki da tsadar rayuwa.
Ko shakka babu, yanzu haka ana cikin wani irin yanayi ne na gwagwagwa da daruruwan wadanda suka kammala makaranta, ba tare da samun aiki yi ba.
Haka zalika, abin la’akari a nan shi ne; idan ilimin da ake da shi ba wani mai zurfi ba ne, za a iya samun mutane da yawa da suke neman aiki.
Amma, idan kuma ilimin mai zurfi ne, wato kamar makarantar gaba da Sakandire, ilimin da aka fi so da yadda aka fara yin sa, akwai yiwuwar samun aiki; ba sai an wani bata lokaci ba, sannan za a iya samun albashi mai tsoka.
Don haka, idan har kana bukatar kasancewa cikin wadanda za a rika yin wawarsu, sakamakon tsayawa da suka yi suka jajirce wajen yin karatu, wajibi ne kai ma ka mayar da hankali a makaranta har sai ka cimma naka burin na karatu.

2. Samun Kudade Ta Hanyoyi Daban-daban
Wadanda suka tsaya suka yi karatu a makarantun gaba da Sakandire tare da samun kwarewa a fannoni daban-daban, na daya daga cikin wadanda za su samu aikin yi; ba tare da shan wuya ba, domin kuwa har daga kasashen waje za a rika rubibin su.
Don haka, A yi kokari wajen yin wannan karatu yadda ya dace tare da samar da lokaci; domin samun irin ilimin da ake bukata, irin haka ne ke sa wa a samu rayuwa mai inganci; wadda kowa da kowa zai yi sha’awar kasancewa cikinta.
Takardunka ko satifiket daban-daban da ka samu, su ne za su yi bayanin ko kai wane ne, su ne kuma za su ja hankalin masu daukar ka aiki. Saboda haka, lallai a yi karatu tukuru a makaranta; duk tsawon lokaci ko shekarun da za a dauka kafin a gama.
Kazalika, ta hanyar duba wannan satifiket ne, masu daukar aiki ke iya gane, wadanda suka mayar da hankali a karatunsu, suka kuma san abin da suke yi.

ADVERTISEMENT

3. Samar Da Ilimin Da Za A Yi Maganin Wasu Matsaloli
Daya daga cikin muhimmancin ilimi shi ne, koya mana yadda za mu samu ilimi tare da yin amfani da shi wajen yin tunani, domin daukar matakin da zai taimaka mana a rayuwarmu.
Kamar yadda aka sani ne, bayan yara sun kammala karatunsu sun samu aiki yi, nauyi tare da matsaloli na hawa kansu ta fuskoki da dama, da farko dai yadda za su biya bashin da suka karba a lokacin sa suna makaranta da yadda za su mallaki gida ko mahalli da kokarin sayen mota da kuma biya wa iyali nasu bukatun da dai sauran makamantansu.
Koda-yake, mutane da dama na shafe shekara da shekaru wajen gwagwarmayar neman wannan ilimi, duk da hakan ya dace a ce suna iya daukar mataki dangane da wasu al’amura nasu. Amma, abin bai tsaya kadai a nan ba, domin kuwa akwai bukatar har sai idan har sun kai ga samun mafita kan matakan da suka dauka; domin samun ingantacciyar rayuwa da kuma ci gaba.

4. Bunkasa Tattalin Arziki
Mafi yawan lokuta, mutanen da suka samu ilimi mai zurfi da nagarta, sun fi samun ayyukan da ake biyan albashi mai tsoka, yadda mutum ya mallaki takardu ko satifiket na ilimi mai zurfi da muhimmanci, irin hakan ne ke bayar da damar samun aiki mai nagarta, inda za a rika ba da albashi mai matukar tsoka.
Har ila yau, ilimi na taimaka wa kasashe wajen samun bunkasa da ci gaban tattalin arziki, sakamakon ilimin da Allah yah ore musu tare da sanin hanyoyin da za su sarrafa shi da kuma yin amfani da shi yadda ya kamata, musamman wajen bunkasa rayuwar al’ummarsu.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Gudunmawa
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.