ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Gudunmawa

Ilimi na matukar bayar da gudunmawa wajen ci gaban al’umma, musamman ma idan ya kasance akwai masu ilimi da dama a cikin al’ummar. Ga dai wasu daga cikin gudunmawar da ilimin ke bayarwa kamar haka:

1. Samar Da Hanyoyin Ayyukan Yi
Samun aikin yi, ba karamin lamari ba ne; musamman a irin halin da ake ciki yanzu na matsalar tattalin arziki da tsadar rayuwa.
Ko shakka babu, yanzu haka ana cikin wani irin yanayi ne na gwagwagwa da daruruwan wadanda suka kammala makaranta, ba tare da samun aiki yi ba.
Haka zalika, abin la’akari a nan shi ne; idan ilimin da ake da shi ba wani mai zurfi ba ne, za a iya samun mutane da yawa da suke neman aiki.
Amma, idan kuma ilimin mai zurfi ne, wato kamar makarantar gaba da Sakandire, ilimin da aka fi so da yadda aka fara yin sa, akwai yiwuwar samun aiki; ba sai an wani bata lokaci ba, sannan za a iya samun albashi mai tsoka.
Don haka, idan har kana bukatar kasancewa cikin wadanda za a rika yin wawarsu, sakamakon tsayawa da suka yi suka jajirce wajen yin karatu, wajibi ne kai ma ka mayar da hankali a makaranta har sai ka cimma naka burin na karatu.

2. Samun Kudade Ta Hanyoyi Daban-daban
Wadanda suka tsaya suka yi karatu a makarantun gaba da Sakandire tare da samun kwarewa a fannoni daban-daban, na daya daga cikin wadanda za su samu aikin yi; ba tare da shan wuya ba, domin kuwa har daga kasashen waje za a rika rubibin su.
Don haka, A yi kokari wajen yin wannan karatu yadda ya dace tare da samar da lokaci; domin samun irin ilimin da ake bukata, irin haka ne ke sa wa a samu rayuwa mai inganci; wadda kowa da kowa zai yi sha’awar kasancewa cikinta.
Takardunka ko satifiket daban-daban da ka samu, su ne za su yi bayanin ko kai wane ne, su ne kuma za su ja hankalin masu daukar ka aiki. Saboda haka, lallai a yi karatu tukuru a makaranta; duk tsawon lokaci ko shekarun da za a dauka kafin a gama.
Kazalika, ta hanyar duba wannan satifiket ne, masu daukar aiki ke iya gane, wadanda suka mayar da hankali a karatunsu, suka kuma san abin da suke yi.

ADVERTISEMENT

3. Samar Da Ilimin Da Za A Yi Maganin Wasu Matsaloli
Daya daga cikin muhimmancin ilimi shi ne, koya mana yadda za mu samu ilimi tare da yin amfani da shi wajen yin tunani, domin daukar matakin da zai taimaka mana a rayuwarmu.
Kamar yadda aka sani ne, bayan yara sun kammala karatunsu sun samu aiki yi, nauyi tare da matsaloli na hawa kansu ta fuskoki da dama, da farko dai yadda za su biya bashin da suka karba a lokacin sa suna makaranta da yadda za su mallaki gida ko mahalli da kokarin sayen mota da kuma biya wa iyali nasu bukatun da dai sauran makamantansu.
Koda-yake, mutane da dama na shafe shekara da shekaru wajen gwagwarmayar neman wannan ilimi, duk da hakan ya dace a ce suna iya daukar mataki dangane da wasu al’amura nasu. Amma, abin bai tsaya kadai a nan ba, domin kuwa akwai bukatar har sai idan har sun kai ga samun mafita kan matakan da suka dauka; domin samun ingantacciyar rayuwa da kuma ci gaba.

4. Bunkasa Tattalin Arziki
Mafi yawan lokuta, mutanen da suka samu ilimi mai zurfi da nagarta, sun fi samun ayyukan da ake biyan albashi mai tsoka, yadda mutum ya mallaki takardu ko satifiket na ilimi mai zurfi da muhimmanci, irin hakan ne ke bayar da damar samun aiki mai nagarta, inda za a rika ba da albashi mai matukar tsoka.
Har ila yau, ilimi na taimaka wa kasashe wajen samun bunkasa da ci gaban tattalin arziki, sakamakon ilimin da Allah yah ore musu tare da sanin hanyoyin da za su sarrafa shi da kuma yin amfani da shi yadda ya kamata, musamman wajen bunkasa rayuwar al’ummarsu.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Gudunmawa
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.