• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Guguwa Mai Karfi Ta Yi Ajalin Mutum 4 A Kasuwar Baje Koli A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Bala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata mummunar guguwa da aka yi a daren ranar Asabar a cikin garin Bauchi ta janyo asarar rayukan mutum hudu a IBB Square inda ake gudanar da kasuwar baje kolin duniya ta arewa maso gabas.

Muhallin IBB square da ke Bauchi dai tsawon makonni ya karbi bakwancin kasuwar baje koli na shiyyar arewa maso gabas inda jihohin da ke shiyyar suka halarta. Guguwar ta yi barna a rumfunan jihar Gombe da Yobe, da kuma tantunan kasuwanci daban-daban da suke cikin kasuwar.

  • Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara
  • Kwamishinan Bauchi Ya Rasu A Hatsarin Mota

A kokarin aikin ceto da ‘yansanda da sauran jami’ai suka yi, sun shiga tantuna da rumfuna domin lalubo wadanda tsautsayin ya rutsa da su inda suka kwashi wadanda suka gamu da barnar zuwa asibiti domin neman kulawar gaggawa na likita.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi, kakakin rundunar ‘yansanda a jihar Bauchi, SP Ahmad Muhammad Wakil, ya ce, mutum biyar ne aka samu a cikin gine-ginen da suka rufta din, inda hudu daga cikinsu suka rasa rayukansu.

Wadanda suka rasa rayukansu din su ne Abdullahi Abubakar, dan shekara 38 da ke unguwar Yakubu Wanka, Sadiq Ahmed Alfa, mai shekara 32 mazaunin unguwar Fadaman Mada, Malam Musa daga Maliya Ventures, Tudun Salmanu da kuma Abdullahi Abdurrahman wanda ya fito daga jihar Gombe.

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

“Mace daya ce taf ta tsira daga cikin mutum 5 da hatsarin guguwar ta shafa wato Fatima Isa ‘yar shekara 31 da ta ke unguwar Inkil a cikin garin Bauchi, wacce a yanzu haka take amsar kulawar likitoci a asibiti.”

Hukumomi dai sun dukufa daukan matakan da suka dace ciki har da kai gawarwakin mamatan zuwa dakin adana gawarwaki da kuma bibiyar irin asarar da aka tafka sakamakon guguwar.

Tunin dai a cewar Wakil, ‘yansanda suka bazama wajen tabbatar da cewa bata-gari ba su yi amfani da wannan damar wajen yi wa ‘yan kasuwan baje kolin sata ba domin tabbatar da kare musu dukiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiGuguwaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Sallah: Tsadar Tumatir Na Barazana Ga Armashin Bikin

Next Post

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Kai Hari Gidan Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano

Related

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

32 minutes ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

3 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

20 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

20 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

21 hours ago
Next Post
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Kai Hari Gidan Shugaban Jam’iyyar APC Na Kano

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Kai Hari Gidan Shugaban Jam'iyyar APC Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.