• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ne Ya Jefa Al’ummar Bauchi Cikin Matsin Rayuwa Ba Tinubu Ba – Sanata Shehu Buba

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Bala Ne Ya Jefa Al’ummar Bauchi Cikin Matsin Rayuwa Ba Tinubu Ba – Sanata Shehu Buba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Mai Wakiltar Mazabar Bauchi ta Kudu, Sanata Shehu Buba Umar, ya ce, suka da caccakar da gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi wa shugaban kasa Bola Tinubu kan matsin rayuwa da ake ciki, ya yi ne kawai domin karkatar da hankulan jama’an jihar daga maƙudan biliyoyin nairori da tulin tirelolin kayan abinci da gwamnatin tarayya ta turo jihar.

 

Ya kuma ce, gwamnatin jihar ta PDP ce ta kakaba wa jama’an jihar yunwa da matsin rayuwa domin gwamnatin tarayya ta bayar da tirelolin shinkafa, taki, dawa domin rabar wa jama’a kyauta, ya zargi gwamnatin jihar da cewa ba ta rabar ba.

  • Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ɗin Masu Hidimar Ƙasa Ba – NYSC
  • Rashin Sani Ne Ya Sa Wasu Ke Karyata Ikirarin Da Na Yi Na Samun Kyautar Motoci 75 -Mai Dawayya

Sanatan ya yi wannan ikirarin ne a yayin da ya ke jawabi a ƙarshen mako yayin bikin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓe da miƙa wa ‘yan takara tuta na zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da kansiloli 323 da zai gudana a jihar Bauchi ranar Asabar 17 ga watan Agusta.

 

Labarai Masu Nasaba

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

Buba ya ce: “Talaucin da ake ta kuka a jihar Bauchi, gwamnatin jihar ce ta assasa mana shi. Bari na gaya mana, ni sanata ne da ke wakiltar Bauchi ta Kudu, duk abon da ake damawa a Abuja a idona ake yi. Ina gaya muku daga 2023 zuwa Janairu, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 144 daga asusun hadaka na tarayya (FAAC), ina waɗannan kuɗaɗen suke? ya fito ya karyata abin da na fada.

 

“Daga watan 1 zuwa yau, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 47, kuma zuwa ƙarshen shekarar nan za ta karɓi kuɗi kimanin naira biliyan 195. Amma yaushe zai zo ya tsaya ya yi ƙarya, ya ce wai gwamnatin APC ta kawo yunwa, balle kai ne kake riƙe da lalitar jihar Bauchi me kake yi wajen kawo sauyi a cikin tsanani da ake ciki?.

Gwamna Bala

“Al’ummar Bauchi su na kallonka kowa yana kallonka. Ina tabbatar muku cewa, yanzu kamar wata shida da suka wuce akwai tirololi na Dawa 70 da aka bayar a kawo wa jihar Bauchi, jihar Bauchi an ba ku? ina ya kai su?. ku tamabaye shi.

 

“Akwai Taki Tireloli 70 da aka bayar a kawo Bauchi kyauta amma yanzu ya zo yana sayar muku a kan naira dubu 50,000. Kwanan nan an bayar da tirelolin Shinkafa 20 don a kawo wa ‘yan jihar Bauchi, ya ba ku?

 

“To, waye ya riƙe kuɗaɗen da kayan abinci da ake kawowa daga gwamantin tarayya?

 

“Kuma kowa ya sani ya je ya ciwo bashi na sama da naira biliyan 300 kuma harƙar hanya ko kwangilar haya shi ya kawo kamfaninsa ne.”

 

Ya ƙara da cewa, “Mu muna zaman lafiya da kai ba mu nemeka da faɗa ba, kai ka tsokano mu ka zage ka, shi ya sa na ce yau za mu biyaka bashi guda ɗaya. Za mu saurareka mu ji amsarka, muna da dozin da za mu amayar wa mutanen jihar Bauchi.”

Gwamna Bala

Shehu Buba da yake magana kan zaɓen, ya tabbatar wa jama’a cewa a shirye APC take, har ma ya bada tabbacin cewa su ne za su lashe zaɓen shugabannin da na kansiloli muddin aka yi adalci.

 

Shi ma a nasa ɓangaren, shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Muhammad Hassan Tilde, ya gargaɗi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi kan yin maguɗi ko taimaka wa PDP da gwamnatin jihar su yi musu maguɗi, ya ce, a shirye suke su kara da kowace jam’iyya kuma su yi nasara.

 

Ya nemi wakilansu da masu sanya ido da su gudanar da ayyukansu yadda ya dace domin daƙile abun da ya kira shirin musu maguɗi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPPDPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Next Post

Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

Related

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

33 minutes ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

3 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

4 hours ago
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

15 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

16 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

18 hours ago
Next Post
Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.