• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ne Ya Jefa Al’ummar Bauchi Cikin Matsin Rayuwa Ba Tinubu Ba – Sanata Shehu Buba

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Gwamna Bala Ne Ya Jefa Al’ummar Bauchi Cikin Matsin Rayuwa Ba Tinubu Ba – Sanata Shehu Buba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Mai Wakiltar Mazabar Bauchi ta Kudu, Sanata Shehu Buba Umar, ya ce, suka da caccakar da gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi wa shugaban kasa Bola Tinubu kan matsin rayuwa da ake ciki, ya yi ne kawai domin karkatar da hankulan jama’an jihar daga maƙudan biliyoyin nairori da tulin tirelolin kayan abinci da gwamnatin tarayya ta turo jihar.

 

Ya kuma ce, gwamnatin jihar ta PDP ce ta kakaba wa jama’an jihar yunwa da matsin rayuwa domin gwamnatin tarayya ta bayar da tirelolin shinkafa, taki, dawa domin rabar wa jama’a kyauta, ya zargi gwamnatin jihar da cewa ba ta rabar ba.

  • Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ɗin Masu Hidimar Ƙasa Ba – NYSC
  • Rashin Sani Ne Ya Sa Wasu Ke Karyata Ikirarin Da Na Yi Na Samun Kyautar Motoci 75 -Mai Dawayya

Sanatan ya yi wannan ikirarin ne a yayin da ya ke jawabi a ƙarshen mako yayin bikin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓe da miƙa wa ‘yan takara tuta na zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da kansiloli 323 da zai gudana a jihar Bauchi ranar Asabar 17 ga watan Agusta.

 

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

Buba ya ce: “Talaucin da ake ta kuka a jihar Bauchi, gwamnatin jihar ce ta assasa mana shi. Bari na gaya mana, ni sanata ne da ke wakiltar Bauchi ta Kudu, duk abon da ake damawa a Abuja a idona ake yi. Ina gaya muku daga 2023 zuwa Janairu, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 144 daga asusun hadaka na tarayya (FAAC), ina waɗannan kuɗaɗen suke? ya fito ya karyata abin da na fada.

 

“Daga watan 1 zuwa yau, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 47, kuma zuwa ƙarshen shekarar nan za ta karɓi kuɗi kimanin naira biliyan 195. Amma yaushe zai zo ya tsaya ya yi ƙarya, ya ce wai gwamnatin APC ta kawo yunwa, balle kai ne kake riƙe da lalitar jihar Bauchi me kake yi wajen kawo sauyi a cikin tsanani da ake ciki?.

Gwamna Bala

“Al’ummar Bauchi su na kallonka kowa yana kallonka. Ina tabbatar muku cewa, yanzu kamar wata shida da suka wuce akwai tirololi na Dawa 70 da aka bayar a kawo wa jihar Bauchi, jihar Bauchi an ba ku? ina ya kai su?. ku tamabaye shi.

 

“Akwai Taki Tireloli 70 da aka bayar a kawo Bauchi kyauta amma yanzu ya zo yana sayar muku a kan naira dubu 50,000. Kwanan nan an bayar da tirelolin Shinkafa 20 don a kawo wa ‘yan jihar Bauchi, ya ba ku?

 

“To, waye ya riƙe kuɗaɗen da kayan abinci da ake kawowa daga gwamantin tarayya?

 

“Kuma kowa ya sani ya je ya ciwo bashi na sama da naira biliyan 300 kuma harƙar hanya ko kwangilar haya shi ya kawo kamfaninsa ne.”

 

Ya ƙara da cewa, “Mu muna zaman lafiya da kai ba mu nemeka da faɗa ba, kai ka tsokano mu ka zage ka, shi ya sa na ce yau za mu biyaka bashi guda ɗaya. Za mu saurareka mu ji amsarka, muna da dozin da za mu amayar wa mutanen jihar Bauchi.”

Gwamna Bala

Shehu Buba da yake magana kan zaɓen, ya tabbatar wa jama’a cewa a shirye APC take, har ma ya bada tabbacin cewa su ne za su lashe zaɓen shugabannin da na kansiloli muddin aka yi adalci.

 

Shi ma a nasa ɓangaren, shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Muhammad Hassan Tilde, ya gargaɗi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi kan yin maguɗi ko taimaka wa PDP da gwamnatin jihar su yi musu maguɗi, ya ce, a shirye suke su kara da kowace jam’iyya kuma su yi nasara.

 

Ya nemi wakilansu da masu sanya ido da su gudanar da ayyukansu yadda ya dace domin daƙile abun da ya kira shirin musu maguɗi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCNNPPPDPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ga ‘Yan Bautar Ƙasa Ba – NYSC

Next Post

Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

6 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

7 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

7 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

10 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

11 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

12 hours ago
Next Post
Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.