ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ne Ya Jefa Al’ummar Bauchi Cikin Matsin Rayuwa Ba Tinubu Ba – Sanata Shehu Buba

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamna Bala

Sanata Mai Wakiltar Mazabar Bauchi ta Kudu, Sanata Shehu Buba Umar, ya ce, suka da caccakar da gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya yi wa shugaban kasa Bola Tinubu kan matsin rayuwa da ake ciki, ya yi ne kawai domin karkatar da hankulan jama’an jihar daga maƙudan biliyoyin nairori da tulin tirelolin kayan abinci da gwamnatin tarayya ta turo jihar.

 

Ya kuma ce, gwamnatin jihar ta PDP ce ta kakaba wa jama’an jihar yunwa da matsin rayuwa domin gwamnatin tarayya ta bayar da tirelolin shinkafa, taki, dawa domin rabar wa jama’a kyauta, ya zargi gwamnatin jihar da cewa ba ta rabar ba.

ADVERTISEMENT
  • Ba Mu Samu Umarnin Ƙara Alawus Ɗin Masu Hidimar Ƙasa Ba – NYSC
  • Rashin Sani Ne Ya Sa Wasu Ke Karyata Ikirarin Da Na Yi Na Samun Kyautar Motoci 75 -Mai Dawayya

Sanatan ya yi wannan ikirarin ne a yayin da ya ke jawabi a ƙarshen mako yayin bikin ƙaddamar da yaƙin neman zaɓe da miƙa wa ‘yan takara tuta na zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da kansiloli 323 da zai gudana a jihar Bauchi ranar Asabar 17 ga watan Agusta.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

Buba ya ce: “Talaucin da ake ta kuka a jihar Bauchi, gwamnatin jihar ce ta assasa mana shi. Bari na gaya mana, ni sanata ne da ke wakiltar Bauchi ta Kudu, duk abon da ake damawa a Abuja a idona ake yi. Ina gaya muku daga 2023 zuwa Janairu, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 144 daga asusun hadaka na tarayya (FAAC), ina waɗannan kuɗaɗen suke? ya fito ya karyata abin da na fada.

 

“Daga watan 1 zuwa yau, jihar Bauchi ta karɓi fiye da naira biliyan 47, kuma zuwa ƙarshen shekarar nan za ta karɓi kuɗi kimanin naira biliyan 195. Amma yaushe zai zo ya tsaya ya yi ƙarya, ya ce wai gwamnatin APC ta kawo yunwa, balle kai ne kake riƙe da lalitar jihar Bauchi me kake yi wajen kawo sauyi a cikin tsanani da ake ciki?.

Gwamna Bala

“Al’ummar Bauchi su na kallonka kowa yana kallonka. Ina tabbatar muku cewa, yanzu kamar wata shida da suka wuce akwai tirololi na Dawa 70 da aka bayar a kawo wa jihar Bauchi, jihar Bauchi an ba ku? ina ya kai su?. ku tamabaye shi.

 

“Akwai Taki Tireloli 70 da aka bayar a kawo Bauchi kyauta amma yanzu ya zo yana sayar muku a kan naira dubu 50,000. Kwanan nan an bayar da tirelolin Shinkafa 20 don a kawo wa ‘yan jihar Bauchi, ya ba ku?

 

“To, waye ya riƙe kuɗaɗen da kayan abinci da ake kawowa daga gwamantin tarayya?

 

“Kuma kowa ya sani ya je ya ciwo bashi na sama da naira biliyan 300 kuma harƙar hanya ko kwangilar haya shi ya kawo kamfaninsa ne.”

 

Ya ƙara da cewa, “Mu muna zaman lafiya da kai ba mu nemeka da faɗa ba, kai ka tsokano mu ka zage ka, shi ya sa na ce yau za mu biyaka bashi guda ɗaya. Za mu saurareka mu ji amsarka, muna da dozin da za mu amayar wa mutanen jihar Bauchi.”

Gwamna Bala

Shehu Buba da yake magana kan zaɓen, ya tabbatar wa jama’a cewa a shirye APC take, har ma ya bada tabbacin cewa su ne za su lashe zaɓen shugabannin da na kansiloli muddin aka yi adalci.

 

Shi ma a nasa ɓangaren, shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi, Muhammad Hassan Tilde, ya gargaɗi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi kan yin maguɗi ko taimaka wa PDP da gwamnatin jihar su yi musu maguɗi, ya ce, a shirye suke su kara da kowace jam’iyya kuma su yi nasara.

 

Ya nemi wakilansu da masu sanya ido da su gudanar da ayyukansu yadda ya dace domin daƙile abun da ya kira shirin musu maguɗi.

Gwamna Bala
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang
  • Sulaiman
    Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris
  • Sulaiman
    Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu
  • Sulaiman
    Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya
Gwamna Bala
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Labarai

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Gwamna Bala
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Gwamna Bala
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Lambar Zinare A Gasar Kwallon Tebur Ta Kungiyoyin Mata A Gasar Olympics Ta Paris

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Gwamna Bala

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
Gwamna Bala

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026
Gwamna Bala

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.