• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Sadaukar Da Albashinsa Da Babura 50 Domin Yaki Da ‘Yan Bindiga A Mahaifarsa.

Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ceton Mutum 39

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamna Bala

Gwamna jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya sha alwashin sadaukar a da Albashinsa na wata-wata domin yakar ayyukan ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane a Mahaifarsa Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar. 

Gwamna Bala ya bayyana hakan ne da yammacin ranar Asabar a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa dangane da garkuwa da aka yi da mutane 39 a Duguri da ke Alkaleri.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

Bala Muhammad, ya jinjina tare da yaba wa hadakar jami’an ‘Yansanda, Sojoji, Jami’an tsaron farin kaya (DSS) da NSCDC tare da hadin guiwar mafarauta bisa ceto mutane 39 da aka yi garkuwa da su a garin Alkaleri.

 

Gwamna Muhammad ya ce, ya sadaukar da albashinsa na wata-wata ne domin a yi  amfani da shi wajen gudanar da ayyukan ‘yan banga da kuma sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da yaki da ‘yan bindiga.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamnan ya kuma sanar da bada kyautar Mashina guda 50 domin yin ayyukan sintiri, da kyautar naira Miliyan 10 ga kungiyar ‘yan banga, tare da naira miliyan biyu ga hakimai biyu da suke yankin domin tabbatar da dakile ‘yan ta’addan da ke garkuwa da mutane a yankin.

Da ya ke nasa jawabin, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Auwal Musa, ya ce, lokacin da suka samu rahoton an yi garkuwa da mutanen, nan take suka hada kai da sauran hukumomin tsaro da mafarauta inda suka kutsa kai dajin Yankari inda maboyar ‘yan ta’addan ta ke, “mun samu nasarar ceto dukkanin wadanda aka yi garkuwa da su, su 39, mun kashe ‘yan ta’adda 10 bayan fafatawa da su”.

Ya jinjina wa gwamnan jihar bisa goyon bayan da yake bayarwa na kyautata harkokin tsaro a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Gwamnatin Kano Ta Yi Jigilar Dalibai 158 Zuwa Jihohi 5 A Karkashin Shirin Musayar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.