• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Bala Ya Sadaukar Da Albashinsa Da Babura 50 Domin Yaki Da ‘Yan Bindiga A Mahaifarsa.

Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ceton Mutum 39

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Bala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya sha alwashin sadaukar a da Albashinsa na wata-wata domin yakar ayyukan ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane a Mahaifarsa Duguri da ke karamar hukumar Alkaleri a jihar. 

Gwamna Bala ya bayyana hakan ne da yammacin ranar Asabar a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa dangane da garkuwa da aka yi da mutane 39 a Duguri da ke Alkaleri.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

Bala Muhammad, ya jinjina tare da yaba wa hadakar jami’an ‘Yansanda, Sojoji, Jami’an tsaron farin kaya (DSS) da NSCDC tare da hadin guiwar mafarauta bisa ceto mutane 39 da aka yi garkuwa da su a garin Alkaleri.

 

Gwamna Muhammad ya ce, ya sadaukar da albashinsa na wata-wata ne domin a yi  amfani da shi wajen gudanar da ayyukan ‘yan banga da kuma sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da yaki da ‘yan bindiga.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Gwamnan ya kuma sanar da bada kyautar Mashina guda 50 domin yin ayyukan sintiri, da kyautar naira Miliyan 10 ga kungiyar ‘yan banga, tare da naira miliyan biyu ga hakimai biyu da suke yankin domin tabbatar da dakile ‘yan ta’addan da ke garkuwa da mutane a yankin.

Da ya ke nasa jawabin, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Auwal Musa, ya ce, lokacin da suka samu rahoton an yi garkuwa da mutanen, nan take suka hada kai da sauran hukumomin tsaro da mafarauta inda suka kutsa kai dajin Yankari inda maboyar ‘yan ta’addan ta ke, “mun samu nasarar ceto dukkanin wadanda aka yi garkuwa da su, su 39, mun kashe ‘yan ta’adda 10 bayan fafatawa da su”.

Ya jinjina wa gwamnan jihar bisa goyon bayan da yake bayarwa na kyautata harkokin tsaro a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandanBauchiGwamnan BauchiYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birnin Shanghai Ya Karbi Bakuncin Bikin Yawon Bude Ido Na 34 Domin Bunkasa Fannin Yawon Shakatawa

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Jigilar Dalibai 158 Zuwa Jihohi 5 A Karkashin Shirin Musayar Dalibai

Related

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

39 minutes ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

9 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

10 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

13 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

15 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

17 hours ago
Next Post
Hajji 2023: Alhazan Nijeriya 6 Sun Rasu, 30 Na Da Tabin Hankali A Saudiyya

Gwamnatin Kano Ta Yi Jigilar Dalibai 158 Zuwa Jihohi 5 A Karkashin Shirin Musayar Dalibai

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.