ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Cafke Dalibai 3, Da Wani Bisa Zargin Shiga Kungiyar Asiri A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
'Yansanda

Hedikwatar rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta sanar da cewa, ta cafke wasu dalibai guda uku da wani mutum daya bisa zarginsu da kasance cikin kungiyar asiri mai suna Black axe.

Wadanda aka kama bisa wannan zargin, su ne, Eric Nuhu mai shekara 23 – dalibi ne da ke matakin karshe a jami’ar ATBU da ke Bauchi; Zaharaddeen Hassan, dan shekara 19, da ke matakin karatu (ND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha ta gwamnatin tarayya da ke Bauchi; Felix John dan shekara 24 – dalibin karatu da ke (HND 1) a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi; da kuma wani mai suna Daniel Masaka dan karamar hukumar Karu a jihar Nasarawa.

  • Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

A sanarwar manema labarai da kakakin ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Muhammad Wakil ya fitar a ranar Juma’a, ya ce, a bisa binciken da suka yi, sun gano cewa, mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin na farko da na biyu sun bayyana cewa, wani abokin karatunsu ne, Abbas Apeh da ke matakin karshe a jami’ar ATBU Bauchi ne ya gayyace su shiga cikin kungiyar a ranar 2 ga watan Satumban 2023.

ADVERTISEMENT

Sauran kuma da ake zargin, sun tabbatar da cewa sun jima da kasancewa mambobin kungiyar asirin ta Black axe.

Ya ce, mambobin kungiyar ne suka gayyacesu domin su halarci wani bikin tarbar amsar sabbin mambobi da aka gudanar a wani waje a Bauchi da ke kusa da matsugunin jami’ar ATBU na dindindin da ke Gubi a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Kano.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Kazalika, a wani labarin makamancin wannan, rundunar ta kuma kama wasu mutum biyu da suka kasance kwararru a bangaren kwacen mashina kuma sun shafe sama da shekaru hudu suna tsula tsiyarsu a cikin kwaryar Bauchi da jihohin makwafta.

A ranar 24 ga watan Agustan, wani mutum mai suna one Aliyu Muhammad Gidado mazaunin unguwar tsohowar Airport inda ya kai rahoto ga ‘yansanda cewa a wannan ranar ya gano wani Bello Mohammed da aka fi sani da Faruk Manja dan shekara 30 mazaunin unguwar Bakaro shi da wani mai suna Kabiru Danfulani da ke Muda Lawal Bauchi (da yanzu ake nema) sun shiga cikin gidansa tare da sace masa mota kirar Honda Civic mai lamba MSA-350-PD da kudinta ya kai naira N640,000;00 tare da wata kwarangwal din mashin hadi da wasu kadarorin da ba a tantance adadinsu ba zuwa yanzu.

Wakil ya ce bayan da suka kaddamar da bincike sun kamo wanda ake zargi da kuma abubuwan da suka sace a lokacin da suke kokarin arcewa.

A cewarsa a lokacin bincike wanda ake zargi na farko ya ce, ya shafe shekaru hudu yana satar mashina kuma zuwa yanzu ya sace mashina za su kai 20 a jihohin Bauchi da Yobe. yayin da shi kuma wanda ake zargi na biyun ya gudu.

Sanarwar ta ce za su gudanar da wadanda suke zargin a gaban kotu da zarar suka kammala gudanar da bincike.

'Yansanda
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

...Ya Kashe Uwargidan Da Yake Yi Wa Hidima Da Mahaifiyarta Gami Da Tafka Sata

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.