• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Buni Ya Gabatar Da Biliyan 163 A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Jihar Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Gwamna Buni Ya Gabatar Da Biliyan 163 A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Jihar Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya gabatar wa zauren majalisar dokokin Jihar Yobe kudurin kasafin kudin 2023 na kimanin N163,155,366,000, domin amincewa. 

Da yake gabatar da kasafin kudin wannan shekara a ranar Alhamis, wanda aka yi wa taken: “Kasafin kudi domin ci gaba daga inda aka tsaya, karfafawa tare da sauya fasalin tattalin arziki” ga zauren majalisar dokokin jihar, Gwamna Buni, ya ce an yi kiyasin kasafin ne domin karfafa nasarorin da ya samu a baya wajen ciyar da jihar gaba.

  • El-rufai Ya Amince Da Nadin Wazirin Garin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Masarautar Jere
  • Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

Kasafin kudin 2023 ya ragu da kashi 0.49 cikin 100, idan aka kwatanta da na shekarar 2022 da ta gabata.

Yayin da a cikin kasafin aka ware N87,800,717,000 wajen gudanar da ayyukan gwamnati na yau da kullum, kimanin kaso 57 cikin 100 na adadin kasafin kudin.

Bugu da kari kuma Gwamna Buni, ya bayyana cewa, an ware jimillar N75,354,649,00 a bangaren manyan ayyukan da gwamnatin jihar za ta aiwatar a wannan shekarar, wanda ya tsaya madadin kaso 43 cikin 100 na kasafin kudin.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Ya kara da cewa kasafin kudin zai karkata ne wajen kammala ayyukan da ake ci gaba da aiwatarwa domin cimma muradun gwamnati wajen farfado da yankunan da rikicin Boko Haram ya tagayyara a jihar, bunkasa harkokin ci gaba da inganta tattalin arziki da walwalar jama’ar jihar.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da kokarin da ta ke wajen gina tituna, da farfado da fannin ilimi da kuma kudirin kammala sauran cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko, a karkashin kudurin gwamnatin jihar na kafa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko guda daya a cikin kowace gunduma daga cikin gundumomi 178 a fadin Jihar Yobe.

A nashi bangare, kakakin Majalisar Dokokin Jihar Yobe, Ahmed Mirwa, ya bayar da tabbacin aiki tukuru wajen ganin zauren majalisar ya duba kasafin kudin tare da amincewa da shi domin bai wa bangaren zartaswa damar gudanarwa da al’ummar Jihar Yobe ayyukan ci gaba, wadanda suke kunshe a cikin kasafin kudin na 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Bunkasa Tattalin ArzikiCi Gaba Da AyyukaJihar YobeKasafin KudiMai Mala Buni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Buni
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.