ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

•Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Joji

Babban Mai Shara’a na Kasa, Justice Olukayode Ariwoola ya gargadi alkalan da aka ware domin jin korafe-korafen zaben 2023 su gudanar da gaskiya da amana wajen zantar da hukunci a kasa kar su kuskura su ci amanan ‘yan Nijeriya a 2023.

Babban mai shari’a na kasa ya bayyana hakan ne a lokacin bude taron bita na kwanaki hadu da aka shirya wa alkalan da za su saurari korafe-korafen zabe a cibiyar shari’a ta kasa da ke Abuja a ranar Litinin da ta gabata.

  • Kotu Ta Kori Sanatan Taraba Daga Kujerarsa Saboda Sauya Sheka Zuwa APC 

Justice Ariwoola ya bukaci jami’an da ke sashin shari’a da su cire duk wata son zuciya wajen gudanar da harkokin shari’a a lokacin da suke yanke hukunci kan a kotuna.
“Ya kamata alkalai su zama masu gaskiya da rukon amana a lokacin da suke zantar da hukunci kan wadanda suka tsaya takara a mukamai daban-daban a zaben 2023, domin su ne masu kwato wa wadanda ba a yi musu adalci ba hakkinsu, sannan ya zama wajibi su yi kokarin sauke nauyin da Allah ya daura musu cikin gaskiya da rikon amana.

ADVERTISEMENT

“Ba a bukatar jami’an da ke sashin shari’a su kasance masu rashin gaskiya wajen gudanar da ayyukansu da ka daura musu, ina mai tabbatar muku da cewa al’umma suna da matukar kwarin gwiwa a kanku wajen yi musu adalci lokacin sauraran karar zabe.
“Gaskiya nauyi ne da ya rataya a wuyanku lokacin da kuke gudanar da ayyukanku na alkalanci, saboda ku kuke amso wa mara karfi hakkinsa ta hanyar gaskiya.

“Dole ku tashi tsaye wajen yakar son zuciya a wurin gudanar da ayyukanku na alkalanci, musamman wajen sauraren korafe-korafen zabe,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Haka ita ma shugaban kotun daukaka kara, Justice Monica Dongban-Mensem ta bayyana cewa alkalan guda 277 wadanda aka zabe domin sauraron korafe-korafen zabe wadanda suka hada da na babban kotun tarayya 4 da kotun sauraron karar ma’aikata ta kasa 3 da na babban kotun Abuja da na jihohi 213 da kotun gargajiya 13 da kotun shari’ar Musulunci 27 da kuma kotun majastiri 17.

Ta bukaci alkalan da su yi kokarin gudanar da aiki bisa kwarewarsu wajen sauke nauyin da aka daura musu.

Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC
A nasa jawabin, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta na kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa a yanzu haka hukumarsa ta shigar da kara 600 daga zaben fid da gwani na jam’iyyun siyasa daban-daban da suka gudanar domin shiga zaben 2023.

Ya kara da cewa hukumarsa ta yi nazarin kan hukunce-hukuncen zaben 2019, musamman wadanda suke kewaye da zabukan gwamnoni da zabukan cike gurbi da aka kammala a wasu yankun wadanda suke bukatar kai kara.

“Cikin makonni biyu da suka gabata, jam’iyya daya kacal mun samu korafi har guda 70 wadanda muka shigar a kotu a cikin mako daya da ke neman amincewa ko sauya ‘yan takara bayan wa’adin da muka saka kan jaddawalin zaben 2023 ya kare.
“An dai kai wasu korafe-korafen zuwa kotun koli,” in ji shi.

Ya zayyano yadda aka samu nasarori a cikin dokar zaben 2022 wanda aka inganta babban zaben 2023, musamman ma samar da na’urorin bayyana sakamakon zabe da hukumar zabe za ta samu nasarar cike gibi a tsakanin dokar zaben 2010.

“Haka kuma, sabon dokar zabe ta bayar da damar shigar da hurimin sauraron kararrakin korafe-korafin gabanin zabe a babban kotun tarayya kan zaben ‘yan takara domin a rage cinkoson a bangaren doka da kuma yin amfani da kotuna ba bisa ka’ida ba wajen yanke hukuncin kan hurumin da kotuna suke da shi,” in ji shi.

Joji
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Joji
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.