• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023

•Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babban Joji Ga Alkalai: Kar Ku Ci Amanar ‘Yan Nijeriya A 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Mai Shara’a na Kasa, Justice Olukayode Ariwoola ya gargadi alkalan da aka ware domin jin korafe-korafen zaben 2023 su gudanar da gaskiya da amana wajen zantar da hukunci a kasa kar su kuskura su ci amanan ‘yan Nijeriya a 2023.

Babban mai shari’a na kasa ya bayyana hakan ne a lokacin bude taron bita na kwanaki hadu da aka shirya wa alkalan da za su saurari korafe-korafen zabe a cibiyar shari’a ta kasa da ke Abuja a ranar Litinin da ta gabata.

  • Kotu Ta Kori Sanatan Taraba Daga Kujerarsa Saboda Sauya Sheka Zuwa APC 

Justice Ariwoola ya bukaci jami’an da ke sashin shari’a da su cire duk wata son zuciya wajen gudanar da harkokin shari’a a lokacin da suke yanke hukunci kan a kotuna.
“Ya kamata alkalai su zama masu gaskiya da rukon amana a lokacin da suke zantar da hukunci kan wadanda suka tsaya takara a mukamai daban-daban a zaben 2023, domin su ne masu kwato wa wadanda ba a yi musu adalci ba hakkinsu, sannan ya zama wajibi su yi kokarin sauke nauyin da Allah ya daura musu cikin gaskiya da rikon amana.

“Ba a bukatar jami’an da ke sashin shari’a su kasance masu rashin gaskiya wajen gudanar da ayyukansu da ka daura musu, ina mai tabbatar muku da cewa al’umma suna da matukar kwarin gwiwa a kanku wajen yi musu adalci lokacin sauraran karar zabe.
“Gaskiya nauyi ne da ya rataya a wuyanku lokacin da kuke gudanar da ayyukanku na alkalanci, saboda ku kuke amso wa mara karfi hakkinsa ta hanyar gaskiya.

“Dole ku tashi tsaye wajen yakar son zuciya a wurin gudanar da ayyukanku na alkalanci, musamman wajen sauraren korafe-korafen zabe,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Haka ita ma shugaban kotun daukaka kara, Justice Monica Dongban-Mensem ta bayyana cewa alkalan guda 277 wadanda aka zabe domin sauraron korafe-korafen zabe wadanda suka hada da na babban kotun tarayya 4 da kotun sauraron karar ma’aikata ta kasa 3 da na babban kotun Abuja da na jihohi 213 da kotun gargajiya 13 da kotun shari’ar Musulunci 27 da kuma kotun majastiri 17.

Ta bukaci alkalan da su yi kokarin gudanar da aiki bisa kwarewarsu wajen sauke nauyin da aka daura musu.

Mun Shigar Da Kara 600 Kan Laifuka Gabanin Zabe – INEC
A nasa jawabin, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta na kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa a yanzu haka hukumarsa ta shigar da kara 600 daga zaben fid da gwani na jam’iyyun siyasa daban-daban da suka gudanar domin shiga zaben 2023.

Ya kara da cewa hukumarsa ta yi nazarin kan hukunce-hukuncen zaben 2019, musamman wadanda suke kewaye da zabukan gwamnoni da zabukan cike gurbi da aka kammala a wasu yankun wadanda suke bukatar kai kara.

“Cikin makonni biyu da suka gabata, jam’iyya daya kacal mun samu korafi har guda 70 wadanda muka shigar a kotu a cikin mako daya da ke neman amincewa ko sauya ‘yan takara bayan wa’adin da muka saka kan jaddawalin zaben 2023 ya kare.
“An dai kai wasu korafe-korafen zuwa kotun koli,” in ji shi.

Ya zayyano yadda aka samu nasarori a cikin dokar zaben 2022 wanda aka inganta babban zaben 2023, musamman ma samar da na’urorin bayyana sakamakon zabe da hukumar zabe za ta samu nasarar cike gibi a tsakanin dokar zaben 2010.

“Haka kuma, sabon dokar zabe ta bayar da damar shigar da hurimin sauraron kararrakin korafe-korafin gabanin zabe a babban kotun tarayya kan zaben ‘yan takara domin a rage cinkoson a bangaren doka da kuma yin amfani da kotuna ba bisa ka’ida ba wajen yanke hukuncin kan hurumin da kotuna suke da shi,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kurar Sauya Fasalin Kudi: ‘Mahaukatan’ Sayen-sayen Da Masu Boye Kudi Ke Yi

Next Post

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 day ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

El-Rufai Ya Nada Wazirin Jere A Matsayin Sabon Sarkin Jere

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.