• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Ƙaddamar Da Fara Rabon Tallafi A Jihar Zamfara

Rabon Ba Na Siyasa Ba Ne, Kowa Zai Amfana

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Dauda Lawal Ya Ƙaddamar Da Fara Rabon Tallafi A Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal, a ranar Talata ya ƙaddamar da rabon kayan abinci a matsayin tallafi ga al’ummar Jihar Zamfara.

Yayin ƙaddamar da wannan bayar da tallafi, Gwamna Lawal ya yi kira ga kwamitin da ke da alhakin rabon tallafin da su yi aiki tsakaninsu da Allah.

  • Gwamna Dauda Ya Karbi ‘Yan Mata Hudu Da Suka Kwashe Watanin 7 A Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Gwamnatin Zamfara Ta Bada Umurnin Ɗaukar ‘Yan Sa-kai

Mai magana da yawun gwamnan na Zamfara, Sulaiman Bala Idris, a wata sanarwar manema labarai da ya fitar a Gusau, ya ce wannan tallafi na daga cikin matakan farko don ragewa mutane raɗaɗin janye tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

Ya ƙara da cewa, gwamnatin tarayya ta bayyana za ta ba jihohi bashin Naira Biliyan 5.

Takardar ta ci gaba da cewa: “A jawabinsa yayin ƙaddamar da tallafin, Gwamna Lawal ya ja hankalin membobin wannan kwamiti da su sa tsoron Allah gaba da komi.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Cikin jawabin, gwamnan ya ce gwamnatin Zamfara za ta ɗauki mataki a kan duk wani wanda aka kama da laifin karkatar da wannan tallafi.

A cikin Naira biliyan 5 da gwamnatin tarayya ta ce za ta ba jihohi bashi, Jihar Zamfara ta samu Naira biliyan biyu, da buhun shinkafa dubu 11, 877 da kuma buhun shinkafa 2, 834, wanda za ta raba su ga ƙananan hukumomi shida.

Sashe na biyu na wannan tallafi za a gabatar da shi ga ƙananan hukumomi takwas wanda za a fara da zaran gwamnatin ta amshi wannan tallafi daga gwamnatin tarayya.

Mataimakin Gwamna, Mallam Mani Mallam Mummuni shi ne zai jagoranci kwamitin da zai yi wannan rabon tallafi ga al’umma.

Kowacce ƙaramar hukuma za ta samu buhun shinkafa 2, 000. Buhunan Taki da amfanin gona.

Haka kuma gwamnatin za ta fara bayar da tallafin karatu ga ɗalibai ‘Yan asalin jihar Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dauda LawalZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

Next Post

Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Sanata Ta Tsige Sanata Jibril Isah Na Mazabar Kogi Ta Gabas

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

30 minutes ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

1 hour ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

10 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

13 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

14 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

14 hours ago
Next Post
Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Sanata Ta Tsige Sanata Jibril Isah Na Mazabar Kogi Ta Gabas

Kotun Sauraren Kararrakin Zaben Sanata Ta Tsige Sanata Jibril Isah Na Mazabar Kogi Ta Gabas

LABARAI MASU NASABA

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.