• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau

by Sulaiman
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Aikin Gina Tashar Mota Ta Zamani A Gusau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na samar da guraben ayyukan yi ga mutanen da rayuwarsu ta dogara ga harkokin tashar mota.

 

A ranar Litinin ne gwamnan ya ƙaddamar da aikin gina tashar mota ta zamani a kan titin Sakkwato zuwa Zariya a Gusau, babban birnin jihar.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, aikin da aka bai wa kamfanin Fieldmark Construction zai haɗa da isassun wuraren ajiye motoci, wuraren hutawa na direbobi, ingantattun na’urorin tsaro, da tsarin bayar da tikitin shiga mota don komai ya zama cikin tsari.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

A jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa aikin wani muhimmin bangare ne na ƙudirin gwamnatinsa na inganta ababen more rayuwa a yankunan Gusau.

 

Ya ƙara da cewa, “Wannan shiri zai inganta tsaro, da inganta samar da kuɗaɗen shiga, da kuma bai wa jiharmu damar yin gogayya da sauran jihohi a faɗin ƙasar nan.

 

“Wannan katafaren tashar motoci ta zamani za ta ƙunshi kayayyakin zamani da aka tsara domin ɗaukar masu ababen hawa na haya da fasinjoji cikin aminci, inganci da tsari.

 

“Sauran muhimman abubuwan da ke cikin wannan aikin sun haɗa da wuraren ajiye motoci da za su nufi kowace jiha, ofishin ‘yan sanda, asibiti, tashar kashe gobara, masallaci, ofishin shuganannin tasha, ofishin ƙungiyar ’yan mota, ban ɗakuna, otel ɗin tasha, wurin lodi, kantin sayar da kayayyaki, wurin zubar da shara, rumbun ajiya, garejin gyaran mota da wurin wankin mota.

 

“A yayin gudanar da aikin, aikin zai ɗauki ƙwararrun ma’aikata da marasa ƙwarewa, kuma da zarar an fara aiki, wurin zai zama cibiyar hada-hadar kasuwanci, wanda zai amfanar da ‘yan kasuwa da masu sauran ayyuka.

 

Gwamnan ya sake tabbatar da cewa samar da muhimman ababen more rayuwa, kamar hanyoyin da gwamnatinsa ta fara ginawa jim kaɗan bayan hawansa mulki – wasu daga cikinsu an ƙaddamar da su ne a yayin bikin cika shekara ɗaya – yana ɗaya daga cikin mafi inganci hanyoyin bunƙasa harkokin kasuwanci da samar wadata a jihar.

 

“Bayan tasirinsa na habaka tattalin arziki, wannan shiri wata hanya ce ta ƙawata babban birnin jiharmu ta hanyar hangen nesa mai zurfi na samar da yanayi na zamani kuma mai inganci ga rayuwar jama’armu.

 

“Da waɗannan kalamai, ina farin cikin ƙaddamar da aikin gina sabuwar tashar mota ta Gusau a hukumance. Allah Subhanahu Wa Ta’ala Ya sanya albarka a wannan aiki, ya kuma sa ya zama silar wadata da ci gaba ga al’ummar Jihar Zamfara.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewa Maso Yammasiyasar NijeriyaTa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Biodun Ya Amince Da ₦70,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Ekiti

Next Post

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

5 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

18 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

1 day ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
Next Post
Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

Zargin Tarayya Da Matar Aure: Miji Ya Ki Amincewa Da Hukuncin Kotun Da Ta Wanke Kwamishinan Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.