• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa ƙa’idojin gudanar da nagartattun ayyukan gwamnati a cikin ma’aikatun gwamnatin jihar.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ƙaddamar da wasu kwamitoci shida domin aiwatar da sauye-sauye da tsare-tsaren samar da sabuwar jihar Zamfara, a tsohon ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma
  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama, Kwamitin Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Kwamitin Amfani da Filaye da Rabon Filaye, da kuma Kwamitin Tsare-tsare na Raya Ƙasa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Samar da Hanyoyin Inganta Rayuwar Al’umma da kuma Kwamitin Bankin Duniya na Magance Matsalar Matsugunai a yankuna.

 

A wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa an aiwatar da hakan ne a tsakani inda aka zaƙulo waɗanda za su yi wannan gagarumin aiki da suka haɗa da Majalisar Zartarwa ta Jihar, Manyan Sakatarori, masu fasaha, malamai, jiga-jigan gudanarwa, da ɗaiɗaikun mutane.

 

“Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama zai kasance ƙarƙashin Mataimakin Gwamna, Mani Mallam Mummini Masarar Mudi, tare da Babban Mai Taimakawa na Musamman a kan Cigaban Al’umma a matsayin Sakatare.

 

“Aikin wannan kwamiti shi ne tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’umma wanda zai inganta ɗorewar ayyukan gwamnati da shirye-shiryen ci gaban bil’adama. Har ila yau, zai daidaita ayyukan ma’aikatu masu alaƙa da bunƙasa ci gaban al’umma da kuma kawar da cikas a cikin ayyuka da dama.

 

“Ta hanyar wannan kwamiti, gwamnati za ta tabbatar da ingantaccen ilimin da jama’armu suka samu, musamman matasa da mata, don ba su damar amfani da ilimin wajen ci gaban al’umma.

 

“Kwamitin na biyu yana da alhakin magance matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a jihar. Wannan kwamiti zai gudanar da cikakken aiki a kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a cikin al’ummominmu, tare da yin nazarin nau’ikan magungunan da ake amfani da su, da ƙididdigar masu amfani da su, da kuma yawan yaɗuwarsa.

 

“Bugu da ƙari, zai binciki tushen abubuwan da ke haifar da shaye-shayen ƙwayoyi tare da ba da shawarar dabarun riga-kafi da shiga tsakani. Uwargidan gwamna, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce za ta shugabanci wannan kwamiti, sannan sakatariyarta za ta kasance daraktar ma’ajin magani na Ma’aikatar Lafiya.

 

“Kwamitin na gaba shi ne wanda zai tabbatar da kammala shirin raya jihar Zamfara na shekaru goma, 2024-2033. Aikin sa shi ne tabbatar da cewa an aiwatar shirin raya jihar wanda aka gabatar watanni biyu da suka gabata, da kuma tabbatar da cewa ya yi daidai da yadda aka tsara.

 

Wannan kwamiti kuma zai samar da hanyoyi cikin harkar gwamnati don cimma maƙasudin shirin. Zai kuma yi aiki kafaɗa da kafaɗa tare da ofishin Hukumar kula da yara ta Duniya UNICEF na yanki da ke Sakkwato domin tsare-tsare, aiwatarwa, amincewa da ƙaddamarwa. Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Malam Wadatau Madawaki ne zai shugabanci wannan kwamitin.

 

“Kwamitin amfani da rabon filaye, shiri ne na dabarbaru, shi ne zai samar da tsarin tafiyar da harkar filaye. Shi ne tattara takardun neman filaye, ya ba Gwamna shawarar waɗanda suka cancanci a ba su filayen, wannan kwamiti ne dai kuma zai bayar da shawarar filayen da za a iya ƙwacewa idan ya yi karo da waɗansu buƙatu.

 

“Bugu da ƙari, wannan kwamiti ne kuma zai tantance biyan diyya ga wuraren da aiki ya bi ta kan su. Gogagge a harkar filaye da safiyo, kuma Tsohon Babban Sakatare, Alhaji Ali Boko ne zai jagoranci wannan kwamiti.

 

“Kwamitin kula da harkokin ‘yan gudun hijira, ‘yan ƙasa, wanda shiri ne na Bankin Duniya ne, Kwamishinan kasafi da tsare-tsare, Abdulmalik Abubakar Gajam ne zai shugabance shi. Wannan kwamiti ne ke da alhakin aiwatar da tsarin Bankin Duniya game da ‘yan gudun hijira da ayyukan ci gaban ƙasa, wanda ma’aikatar kasa da tsare-tsaren tattalin arziki ta tarayya ke jagoranta.

 

“An samar da wannan shiri ne don inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da ‘yan ƙasa a yankunan Ƙananan Hukumomin da abin ya shafa a Arewacin Nijeriya, wanda jihar Zamfara na ciki.

 

“Kwamiti na ƙarshe da aka ƙaddamar shi ne Kwamitin samar da hanyoyin inganta rayuwar ɗan adam don ci gaba, da kuma daidaito a harkar gwamnati.

 

“Wannan wani bangare ne na shirin kasa da jihar Zamfara ke da niyyar gudanarwa.

 

Wannan shirin ya ƙunshi ayyuka guda uku masu dogaro da juna waɗanda aka tsara don magance ƙalubale daban-daban da tallafawa da kuma rarraba albarkatu da haɓaka kashe kuɗi don ilimin firamare da ayyukan kiwon lafiya a matakin farko.

 

Kwamitin zai mayar da hankali kan ƙara samar da inganci na samar da kuɗaɗe don ilimin firamare da kiwon lafiya, inganta gaskiya da riƙon amana, da inganta ɗaukar ma’aikata da gudanar da ayyukan malamai da ma’aikatan kiwon lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma

Next Post

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Related

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

9 minutes ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

12 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

13 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

14 hours ago
Next Post
Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

LABARAI MASU NASABA

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.