• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa ƙa’idojin gudanar da nagartattun ayyukan gwamnati a cikin ma’aikatun gwamnatin jihar.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ƙaddamar da wasu kwamitoci shida domin aiwatar da sauye-sauye da tsare-tsaren samar da sabuwar jihar Zamfara, a tsohon ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma
  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama, Kwamitin Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Kwamitin Amfani da Filaye da Rabon Filaye, da kuma Kwamitin Tsare-tsare na Raya Ƙasa.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Samar da Hanyoyin Inganta Rayuwar Al’umma da kuma Kwamitin Bankin Duniya na Magance Matsalar Matsugunai a yankuna.

 

A wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa an aiwatar da hakan ne a tsakani inda aka zaƙulo waɗanda za su yi wannan gagarumin aiki da suka haɗa da Majalisar Zartarwa ta Jihar, Manyan Sakatarori, masu fasaha, malamai, jiga-jigan gudanarwa, da ɗaiɗaikun mutane.

 

“Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama zai kasance ƙarƙashin Mataimakin Gwamna, Mani Mallam Mummini Masarar Mudi, tare da Babban Mai Taimakawa na Musamman a kan Cigaban Al’umma a matsayin Sakatare.

 

“Aikin wannan kwamiti shi ne tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’umma wanda zai inganta ɗorewar ayyukan gwamnati da shirye-shiryen ci gaban bil’adama. Har ila yau, zai daidaita ayyukan ma’aikatu masu alaƙa da bunƙasa ci gaban al’umma da kuma kawar da cikas a cikin ayyuka da dama.

 

“Ta hanyar wannan kwamiti, gwamnati za ta tabbatar da ingantaccen ilimin da jama’armu suka samu, musamman matasa da mata, don ba su damar amfani da ilimin wajen ci gaban al’umma.

 

“Kwamitin na biyu yana da alhakin magance matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a jihar. Wannan kwamiti zai gudanar da cikakken aiki a kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a cikin al’ummominmu, tare da yin nazarin nau’ikan magungunan da ake amfani da su, da ƙididdigar masu amfani da su, da kuma yawan yaɗuwarsa.

 

“Bugu da ƙari, zai binciki tushen abubuwan da ke haifar da shaye-shayen ƙwayoyi tare da ba da shawarar dabarun riga-kafi da shiga tsakani. Uwargidan gwamna, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce za ta shugabanci wannan kwamiti, sannan sakatariyarta za ta kasance daraktar ma’ajin magani na Ma’aikatar Lafiya.

 

“Kwamitin na gaba shi ne wanda zai tabbatar da kammala shirin raya jihar Zamfara na shekaru goma, 2024-2033. Aikin sa shi ne tabbatar da cewa an aiwatar shirin raya jihar wanda aka gabatar watanni biyu da suka gabata, da kuma tabbatar da cewa ya yi daidai da yadda aka tsara.

 

Wannan kwamiti kuma zai samar da hanyoyi cikin harkar gwamnati don cimma maƙasudin shirin. Zai kuma yi aiki kafaɗa da kafaɗa tare da ofishin Hukumar kula da yara ta Duniya UNICEF na yanki da ke Sakkwato domin tsare-tsare, aiwatarwa, amincewa da ƙaddamarwa. Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Malam Wadatau Madawaki ne zai shugabanci wannan kwamitin.

 

“Kwamitin amfani da rabon filaye, shiri ne na dabarbaru, shi ne zai samar da tsarin tafiyar da harkar filaye. Shi ne tattara takardun neman filaye, ya ba Gwamna shawarar waɗanda suka cancanci a ba su filayen, wannan kwamiti ne dai kuma zai bayar da shawarar filayen da za a iya ƙwacewa idan ya yi karo da waɗansu buƙatu.

 

“Bugu da ƙari, wannan kwamiti ne kuma zai tantance biyan diyya ga wuraren da aiki ya bi ta kan su. Gogagge a harkar filaye da safiyo, kuma Tsohon Babban Sakatare, Alhaji Ali Boko ne zai jagoranci wannan kwamiti.

 

“Kwamitin kula da harkokin ‘yan gudun hijira, ‘yan ƙasa, wanda shiri ne na Bankin Duniya ne, Kwamishinan kasafi da tsare-tsare, Abdulmalik Abubakar Gajam ne zai shugabance shi. Wannan kwamiti ne ke da alhakin aiwatar da tsarin Bankin Duniya game da ‘yan gudun hijira da ayyukan ci gaban ƙasa, wanda ma’aikatar kasa da tsare-tsaren tattalin arziki ta tarayya ke jagoranta.

 

“An samar da wannan shiri ne don inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da ‘yan ƙasa a yankunan Ƙananan Hukumomin da abin ya shafa a Arewacin Nijeriya, wanda jihar Zamfara na ciki.

 

“Kwamiti na ƙarshe da aka ƙaddamar shi ne Kwamitin samar da hanyoyin inganta rayuwar ɗan adam don ci gaba, da kuma daidaito a harkar gwamnati.

 

“Wannan wani bangare ne na shirin kasa da jihar Zamfara ke da niyyar gudanarwa.

 

Wannan shirin ya ƙunshi ayyuka guda uku masu dogaro da juna waɗanda aka tsara don magance ƙalubale daban-daban da tallafawa da kuma rarraba albarkatu da haɓaka kashe kuɗi don ilimin firamare da ayyukan kiwon lafiya a matakin farko.

 

Kwamitin zai mayar da hankali kan ƙara samar da inganci na samar da kuɗaɗe don ilimin firamare da kiwon lafiya, inganta gaskiya da riƙon amana, da inganta ɗaukar ma’aikata da gudanar da ayyukan malamai da ma’aikatan kiwon lafiya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma

Next Post

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

2 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

4 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

19 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

19 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

20 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

21 hours ago
Next Post
Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.