ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa ƙa’idojin gudanar da nagartattun ayyukan gwamnati a cikin ma’aikatun gwamnatin jihar.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ƙaddamar da wasu kwamitoci shida domin aiwatar da sauye-sauye da tsare-tsaren samar da sabuwar jihar Zamfara, a tsohon ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma
  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama, Kwamitin Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Kwamitin Amfani da Filaye da Rabon Filaye, da kuma Kwamitin Tsare-tsare na Raya Ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Samar da Hanyoyin Inganta Rayuwar Al’umma da kuma Kwamitin Bankin Duniya na Magance Matsalar Matsugunai a yankuna.

 

A wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa an aiwatar da hakan ne a tsakani inda aka zaƙulo waɗanda za su yi wannan gagarumin aiki da suka haɗa da Majalisar Zartarwa ta Jihar, Manyan Sakatarori, masu fasaha, malamai, jiga-jigan gudanarwa, da ɗaiɗaikun mutane.

 

“Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama zai kasance ƙarƙashin Mataimakin Gwamna, Mani Mallam Mummini Masarar Mudi, tare da Babban Mai Taimakawa na Musamman a kan Cigaban Al’umma a matsayin Sakatare.

 

“Aikin wannan kwamiti shi ne tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’umma wanda zai inganta ɗorewar ayyukan gwamnati da shirye-shiryen ci gaban bil’adama. Har ila yau, zai daidaita ayyukan ma’aikatu masu alaƙa da bunƙasa ci gaban al’umma da kuma kawar da cikas a cikin ayyuka da dama.

 

“Ta hanyar wannan kwamiti, gwamnati za ta tabbatar da ingantaccen ilimin da jama’armu suka samu, musamman matasa da mata, don ba su damar amfani da ilimin wajen ci gaban al’umma.

 

“Kwamitin na biyu yana da alhakin magance matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a jihar. Wannan kwamiti zai gudanar da cikakken aiki a kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a cikin al’ummominmu, tare da yin nazarin nau’ikan magungunan da ake amfani da su, da ƙididdigar masu amfani da su, da kuma yawan yaɗuwarsa.

 

“Bugu da ƙari, zai binciki tushen abubuwan da ke haifar da shaye-shayen ƙwayoyi tare da ba da shawarar dabarun riga-kafi da shiga tsakani. Uwargidan gwamna, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce za ta shugabanci wannan kwamiti, sannan sakatariyarta za ta kasance daraktar ma’ajin magani na Ma’aikatar Lafiya.

 

“Kwamitin na gaba shi ne wanda zai tabbatar da kammala shirin raya jihar Zamfara na shekaru goma, 2024-2033. Aikin sa shi ne tabbatar da cewa an aiwatar shirin raya jihar wanda aka gabatar watanni biyu da suka gabata, da kuma tabbatar da cewa ya yi daidai da yadda aka tsara.

 

Wannan kwamiti kuma zai samar da hanyoyi cikin harkar gwamnati don cimma maƙasudin shirin. Zai kuma yi aiki kafaɗa da kafaɗa tare da ofishin Hukumar kula da yara ta Duniya UNICEF na yanki da ke Sakkwato domin tsare-tsare, aiwatarwa, amincewa da ƙaddamarwa. Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Malam Wadatau Madawaki ne zai shugabanci wannan kwamitin.

 

“Kwamitin amfani da rabon filaye, shiri ne na dabarbaru, shi ne zai samar da tsarin tafiyar da harkar filaye. Shi ne tattara takardun neman filaye, ya ba Gwamna shawarar waɗanda suka cancanci a ba su filayen, wannan kwamiti ne dai kuma zai bayar da shawarar filayen da za a iya ƙwacewa idan ya yi karo da waɗansu buƙatu.

 

“Bugu da ƙari, wannan kwamiti ne kuma zai tantance biyan diyya ga wuraren da aiki ya bi ta kan su. Gogagge a harkar filaye da safiyo, kuma Tsohon Babban Sakatare, Alhaji Ali Boko ne zai jagoranci wannan kwamiti.

 

“Kwamitin kula da harkokin ‘yan gudun hijira, ‘yan ƙasa, wanda shiri ne na Bankin Duniya ne, Kwamishinan kasafi da tsare-tsare, Abdulmalik Abubakar Gajam ne zai shugabance shi. Wannan kwamiti ne ke da alhakin aiwatar da tsarin Bankin Duniya game da ‘yan gudun hijira da ayyukan ci gaban ƙasa, wanda ma’aikatar kasa da tsare-tsaren tattalin arziki ta tarayya ke jagoranta.

 

“An samar da wannan shiri ne don inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da ‘yan ƙasa a yankunan Ƙananan Hukumomin da abin ya shafa a Arewacin Nijeriya, wanda jihar Zamfara na ciki.

 

“Kwamiti na ƙarshe da aka ƙaddamar shi ne Kwamitin samar da hanyoyin inganta rayuwar ɗan adam don ci gaba, da kuma daidaito a harkar gwamnati.

 

“Wannan wani bangare ne na shirin kasa da jihar Zamfara ke da niyyar gudanarwa.

 

Wannan shirin ya ƙunshi ayyuka guda uku masu dogaro da juna waɗanda aka tsara don magance ƙalubale daban-daban da tallafawa da kuma rarraba albarkatu da haɓaka kashe kuɗi don ilimin firamare da ayyukan kiwon lafiya a matakin farko.

 

Kwamitin zai mayar da hankali kan ƙara samar da inganci na samar da kuɗaɗe don ilimin firamare da kiwon lafiya, inganta gaskiya da riƙon amana, da inganta ɗaukar ma’aikata da gudanar da ayyukan malamai da ma’aikatan kiwon lafiya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Labarai

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
Next Post
Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

LABARAI MASU NASABA

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025
Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

November 11, 2025
Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

Jakadun Kasashen Waje: Shirin Raya Kasa Na 15 Na Sin Na Dauke Da Kyakkyawan Sako

November 11, 2025
APC

Sauya Sheƙa: Yadda APC Ke Ci Gaba Da Hamɓarar Da Jam’iyyun Adawa A Majalisa

November 11, 2025
An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

An Kaddamar Da Babbar Hanyar Mota Da Sin Ta Tallafa Wajen Ginawa A Namibia

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.