ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Kwamitoci Shida Domin Ƙara Inganta Jihar Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na kafa ƙa’idojin gudanar da nagartattun ayyukan gwamnati a cikin ma’aikatun gwamnatin jihar.

 

A ranar Alhamis ne gwamnan ya ƙaddamar da wasu kwamitoci shida domin aiwatar da sauye-sauye da tsare-tsaren samar da sabuwar jihar Zamfara, a tsohon ɗakin taro na gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kawo Karshen Ayyukan ‘Yan Ta’adda A Arewa Maso Yamma
  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama, Kwamitin Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, Kwamitin Amfani da Filaye da Rabon Filaye, da kuma Kwamitin Tsare-tsare na Raya Ƙasa.

 

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran kwamitocin da aka ƙaddamar sun haɗa da Kwamitin Samar da Hanyoyin Inganta Rayuwar Al’umma da kuma Kwamitin Bankin Duniya na Magance Matsalar Matsugunai a yankuna.

 

A wajen ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa an aiwatar da hakan ne a tsakani inda aka zaƙulo waɗanda za su yi wannan gagarumin aiki da suka haɗa da Majalisar Zartarwa ta Jihar, Manyan Sakatarori, masu fasaha, malamai, jiga-jigan gudanarwa, da ɗaiɗaikun mutane.

 

“Kwamitin Inganta Rayuwar Bil’adama zai kasance ƙarƙashin Mataimakin Gwamna, Mani Mallam Mummini Masarar Mudi, tare da Babban Mai Taimakawa na Musamman a kan Cigaban Al’umma a matsayin Sakatare.

 

“Aikin wannan kwamiti shi ne tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da al’umma wanda zai inganta ɗorewar ayyukan gwamnati da shirye-shiryen ci gaban bil’adama. Har ila yau, zai daidaita ayyukan ma’aikatu masu alaƙa da bunƙasa ci gaban al’umma da kuma kawar da cikas a cikin ayyuka da dama.

 

“Ta hanyar wannan kwamiti, gwamnati za ta tabbatar da ingantaccen ilimin da jama’armu suka samu, musamman matasa da mata, don ba su damar amfani da ilimin wajen ci gaban al’umma.

 

“Kwamitin na biyu yana da alhakin magance matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a jihar. Wannan kwamiti zai gudanar da cikakken aiki a kan daƙile shaye-shayen miyagun ƙwayoyi a cikin al’ummominmu, tare da yin nazarin nau’ikan magungunan da ake amfani da su, da ƙididdigar masu amfani da su, da kuma yawan yaɗuwarsa.

 

“Bugu da ƙari, zai binciki tushen abubuwan da ke haifar da shaye-shayen ƙwayoyi tare da ba da shawarar dabarun riga-kafi da shiga tsakani. Uwargidan gwamna, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce za ta shugabanci wannan kwamiti, sannan sakatariyarta za ta kasance daraktar ma’ajin magani na Ma’aikatar Lafiya.

 

“Kwamitin na gaba shi ne wanda zai tabbatar da kammala shirin raya jihar Zamfara na shekaru goma, 2024-2033. Aikin sa shi ne tabbatar da cewa an aiwatar shirin raya jihar wanda aka gabatar watanni biyu da suka gabata, da kuma tabbatar da cewa ya yi daidai da yadda aka tsara.

 

Wannan kwamiti kuma zai samar da hanyoyi cikin harkar gwamnati don cimma maƙasudin shirin. Zai kuma yi aiki kafaɗa da kafaɗa tare da ofishin Hukumar kula da yara ta Duniya UNICEF na yanki da ke Sakkwato domin tsare-tsare, aiwatarwa, amincewa da ƙaddamarwa. Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Malam Wadatau Madawaki ne zai shugabanci wannan kwamitin.

 

“Kwamitin amfani da rabon filaye, shiri ne na dabarbaru, shi ne zai samar da tsarin tafiyar da harkar filaye. Shi ne tattara takardun neman filaye, ya ba Gwamna shawarar waɗanda suka cancanci a ba su filayen, wannan kwamiti ne dai kuma zai bayar da shawarar filayen da za a iya ƙwacewa idan ya yi karo da waɗansu buƙatu.

 

“Bugu da ƙari, wannan kwamiti ne kuma zai tantance biyan diyya ga wuraren da aiki ya bi ta kan su. Gogagge a harkar filaye da safiyo, kuma Tsohon Babban Sakatare, Alhaji Ali Boko ne zai jagoranci wannan kwamiti.

 

“Kwamitin kula da harkokin ‘yan gudun hijira, ‘yan ƙasa, wanda shiri ne na Bankin Duniya ne, Kwamishinan kasafi da tsare-tsare, Abdulmalik Abubakar Gajam ne zai shugabance shi. Wannan kwamiti ne ke da alhakin aiwatar da tsarin Bankin Duniya game da ‘yan gudun hijira da ayyukan ci gaban ƙasa, wanda ma’aikatar kasa da tsare-tsaren tattalin arziki ta tarayya ke jagoranta.

 

“An samar da wannan shiri ne don inganta rayuwar ‘yan gudun hijira da ‘yan ƙasa a yankunan Ƙananan Hukumomin da abin ya shafa a Arewacin Nijeriya, wanda jihar Zamfara na ciki.

 

“Kwamiti na ƙarshe da aka ƙaddamar shi ne Kwamitin samar da hanyoyin inganta rayuwar ɗan adam don ci gaba, da kuma daidaito a harkar gwamnati.

 

“Wannan wani bangare ne na shirin kasa da jihar Zamfara ke da niyyar gudanarwa.

 

Wannan shirin ya ƙunshi ayyuka guda uku masu dogaro da juna waɗanda aka tsara don magance ƙalubale daban-daban da tallafawa da kuma rarraba albarkatu da haɓaka kashe kuɗi don ilimin firamare da ayyukan kiwon lafiya a matakin farko.

 

Kwamitin zai mayar da hankali kan ƙara samar da inganci na samar da kuɗaɗe don ilimin firamare da kiwon lafiya, inganta gaskiya da riƙon amana, da inganta ɗaukar ma’aikata da gudanar da ayyukan malamai da ma’aikatan kiwon lafiya.”

Gwamna lawal
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Gwamna lawal
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

Dan Jarida Ya Kirkiro Manhajar Bincike Ta Hausa

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.