• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Majalisar Zartaswa Kan Tattara Kudin Fansho

bySadiq
2 years ago
Lawal

A ranar Litinin ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwa ta jihar Zamfara.

A wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya karbi bayani daga kwamitin da aka kafa domin tabbatar da matsayin kudaden fansho na jihar Zamfara da na kananan hukumomi.

  • Rikicin Ribas: Tinubu Ya Shiga Tsakanin Fubara Da Wike
  • Babu Shirin Sake Sauya Fasalin Naira — CBN

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce taron da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnati da ke Gusau, an tattauna batutuwan da suka shafi ci gaban jihar Zamfara.

Ya kara da cewa majalisar ta samu rahoton ci gaban da aka samu na shirin ingantawa da zamanantar da filin wasa na tunawa da Sardauna Gusau da dai sauransu.

Ya ce: “A ranar 9 ga Oktoba, 2023, Majalisar zartaswa ta Jihar Zamfara ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin Shugaban Ma’aikata, domin tantance matsayin da Jihar Zamfara ta ke da shi na bayar da gudunmawar fansho na kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Yayin da yake yi wa majalisar bayani, Shugaban kwamitin kuma shugaban ma’aikata na jihar Zamfara Ahmad Aliyu Liman ya bayyana cewa manufar kwamitin ita ce ta binciki zargin karkatar da kudaden da aka zaftare daga albashin ma’aikatan jiha da na kananan hukumomin jihar kan shirinsu na fansho.

“Wadannan kudade ya kamata a mika su ga masu kula da asusun fansho (PFAs) wadanda ke da alhakin kula da asusun ajiyar ma’aikata (RSAs) a jihar.

“Shugaban kwamatin ya bayyana cewa rashin fitar da kudaden ya saba wa dokar fansho ta (2014) da ke tafiyar da tsarin tafiyar da kudaden fansho kamar yadda hukumar fansho ta kasa (PenCom) ta tsara.

“Ya kuma kara nanata cewa rashin kudin da aka samu ya haifar da gazawar Hukumar Kula da Kudaden Fansho (PFAs) ta kasa biyan kudin fansho da na wadanda suka mutu yadda ya dace, wanda hakan ya haifar da koma baya ga kudaden da ba a biya ba a halin yanzu ya yi wa Gwamnatin Jiha yawa.

“Gwamna Lawal a matsayinsa na Shugaban Majalisar Zartaswa, ya bayyana aniyar bayar da tallafin da ya dace don kai dauki ga duk wani abu da ba a biya ba,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version