• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jinjina Wa Obaseki Kan Shirin Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Edo 

by Sulaiman
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Jinjina Wa Obaseki Kan Shirin Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Edo 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa Gwamna Godwin Obaseki kan yadda ya kawo sauyi da kuma ƙudirinsa na inganta fannin kiwon lafiya a Jihar Edo.

 

Gwamnan ya kasance babban baƙo a wajen bikin ƙaddamarwa, rantsar da sababbin ɗalibai da kuma cika shekaru 60 da kafa Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya da Fasaha ta Edo (EdoCOHEST) da aka gudanar a birnin Benin a ranar Larabar da ta gabata.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Da Ministoci 7 Da Tinubu Ya Nada
  • ‘Yan Bindiga Ba Su Karɓe Sansanin Horo Da Ke Neja Ba – Hedikwatar Tsaro

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa bayan ƙaddamar da kwalejin, gwamnonin sun zagaya da kayayyakin zamani da aka samar a ginin.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

A lokacin da yake gabatar da jawabinsa, Gwamna Lawal ya ba da shawarar cewa jihohin biyu su kafa shirin musayar ɗalibai, wanda zai bai wa ɗalibai mata da ke makarantun kiwon lafiya a Zamfara damar zuwa kwalejin Edo domin yin wani zagon karatu.

Gwamna lawal

Ya ce, “Haƙiƙa babban abin alfahari ne da kuma gata kasancewata a nan wurin tare da ɗan uwana da mutanen kirki na jihar Edo don buɗe wani sabon babi na Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiyar da Fasaha ta Edo, musamman ga ɗaliban da suka shigo yanzu.

 

“Yayin da muka taru a nan, ina jinjina irin hangen nesa da jajircewar ɗan uwana Gwamna Obaseki, wanda ya sake farfaɗo da fata a Jihar Edo cikin kyakkyawar manufa, za a iya samun ɗaukaka duk da rashin daidaito a ƙasarmu mai albarka.

 

“Lokacin da na samu bayanai game da wannan ingantaccen aikin gaba ɗaya, na yaba kuma na jinjina wa ɗan uwana kan irin wannan manufa da za a iya cimmawa kaɗai ta bangaren juriya, hangen nesa da sadaukarwa.

 

“Ga ɗaliban da suka shigo a yau, zan ce ku ne burinmu kuma alfaharinmu. Kuna wakiltar jihar Edo da ƙasar mu gaba ɗaya ne. Don haka kada ku iyakance kanka.

 

“Ku yi karatu kuma ku yi fice a karatun; ku daraja aikin da ɗan uwana ya yi a yau don kanku da ɗalibai a nan gaba.

Gwamna lawal

“Baya ga samar da ƙwararrun masana kiwon lafiya, ina addu’a cewa wannan kwaleji ta zama wata gada ta haɗa kan jama’a, samar da ayyukan yi, da bunƙasar tattalin arziki a ciki da wajen jihar Edo. ”

 

Gwamna Obaseki ya gode wa Gwamna Lawal bisa girmama gayyatar da mutanen jihar Edo suka yi masa.

 

“Ina matuƙar godiya da kai ɗan uwana Gwamnan Jihar Zamfara, Dokta Dauda Lawal da ka zo min wannan biki mai bangarori uku, wanda ya hada da ƙaddamarwa, rantsar da sabbin ɗalibai, da kuma cika shekaru 60 da kafa Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya da Fasaha ta Edo (EdoCOHEST).”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kiwon LafiyaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume

Next Post

Gwamna Sani Ya Amince Da ₦72,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Jihar Kaduna 

Related

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza
Manyan Labarai

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

13 minutes ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

56 minutes ago
Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

1 hour ago
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

11 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

15 hours ago
Next Post
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Amince Da ₦72,000 Mafi Ƙarancin Albashi Ga Ma’aikatan Jihar Kaduna 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

Tinubu Zai Tarbi Gawar Buhari A Daura Don Yi Mata Jana’iza

July 15, 2025
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima

July 15, 2025
Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

Sojoji Sun Daƙile Satar Mai, Sun Kama Mutane 50 A Neja Delta

July 15, 2025
Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.