• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Ortom Ya Bukaci A Saki Jagoran IPOB Nnamdi Kanu

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Gwamna Ortom Ya Bukaci A Saki Jagoran IPOB Nnamdi Kanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Binuwai, ya yi kira da a sake Shugaban haramtacciyar kungiyar gwagwarmayar kafa yankin Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, da ake tsare da shi a halin yanzu domin daukar matakin zaman lafiya da muhimmancin gaske a kasar nan.

Gwamna Ortom ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya amshi bakwancin wasu ‘yan asalin Igbo karkashin ‘American Veterans of Igbo Origin’ da suka kai masa ziyarar a Washington DC, da ke kasar Amurka ranar Laraba.

  • Okupe Ya Janye A Matsayin Dan Takarar Mataimakin Jam’iyyar Labour Ta Peter Obi

Ya ce, batun Kanu kalubale ne da ya shafi zamantakewa da siyasa don haka akwai bukatar tafiyar da lamarin cikin siyasa domin shawo kan kalubalen.

Gwamnan ya ce hatta mambobin Boko Haram da suka zama barazana ga tsaron kasa ana samun wadanda aka ‘yantasu har ma su koma cikin al’umma tare da zargi cewa har ma shiga aikin soja su na yi.

Gwamna Ortom ya ce akwai bukatar bai wa yankin Kudu Maso Gabas damar jin an tare da su ta hanyar sauraron kullin da ke ransu na ganin wariya ga wani bangare a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Ya jawo hankalin tsoffin ‘yan Igbo da suke zaure a Amurka da su cewa Nijeriya daya ce, ya duk duniya babu kasar da bata da kalubalen da ke damunta.

Ortom ya shaida wa kungiyar cewa mulkin Nijeriya zai dawo yankin Kudu Maso Gabas ne kawai idan al’ummar yankin suka jingine banbance-banbancensu waje guda suka hada kai domin cigabansu.

Gwamnan ya gode wa kungiyar a bisa gudunmawar da suke bayarwa ya kuma nemi da su cigaba da bada gudunmawarsu wajen kyautata zaman lafiya a Nijeriya.

Kungiyar a karkashin jagorancin Shugabanta Dakta Sylvester Onyia, da mataimakinsa Dakta Prince Joe Nduka.

Sauran mambobin da suka kai ziyarar sun hada da Dr Ofo, Kakakin kungiyar, tsohon Jakadan Nijeriya a Afirka ta Kudu Dr Mrs Ajulu.

Onyia ya jinjina wa Ortom a bisa kokarinsa, ya nuna cewa irin su Ortom Nijeriya take bukata a matsayin shugabanni. Ya ce, duk da suna kasar waje amma suna nazartar abubuwan da suke faruwa a Nijeriya.

Daga nan ya nuna fargana kan zaben 2023 da cewa matsalolin tsaro da suke faruwa a Nijeriya kada su kai ga kawo matsala ga babban zaben.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IPOB Ta Yi Barazana Ga Jakadiyar Birtaniya A Nijeriya

Next Post

Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya – Buhari

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

3 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

11 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

13 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

14 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

15 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

18 hours ago
Next Post
Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya – Buhari

Ya Kamata A Kafa Kotun Hukunta Masu Cin Hanci Da Rashawa Ta Duniya - Buhari

LABARAI MASU NASABA

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.