• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Raɗɗa Ya Raba Naira Miliyan 20 Ga Iyalan ‘Yan Sintirin Da Suka Rasu A Yaki Da ‘Yan Bindiga

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Radda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ware kuɗi naira miliyan 20 domin tallafawa iyalan ‘yan sintiri da suka rasa rayukansu a lokacin fafatawa da ‘yan bindiga.

 

Da yake ƙaddamar da bada wannan tallafi, sakataren gwamnatin jihar Katsina Alhaji Abdullahi Garba Faskari ya bayyana cewa, anyi wannan tsari da kyakkyawar niyya domin rage radadin rashin da iyalan jami’an tsaro da ‘yan sintiri suka yi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

A cewar sa wannan ɗaya ne daga cikin tarin tsare-tsaren da wannan gwamnati take da shi na nuna kauna da tausaya wa ga iyalan waɗanda suka rasa iyalansu da kuma waɗanda suka samu raunuka.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Sakataren gwamnatin jihar Katsina ya ƙara da cewa wannan yana daga cikin alkawarin da gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ya ɗauka akan wannan matsala ta tsaro wanda ya ce kullum da abin yake kwana da shi yake tashin.

 

“Idan jama’a ba su manta ba, gwamna Malam Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa idan kuɗin jihar Katsina za su ƙare akan matsalar tsaro, to zai tunkare ta tsakaninsa da Allah, kuma ku shaida ne, kwana nan ya amince da kashe Naira biliyan dubu 7.8 akan wannan matsala.” Inji Faskari

 

Haka kuma ya yi kira ga jama’a da su taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri wanda zai taimaka wajan kawo ƙarshen wannan matsala, sannan ya ƙara jaddada cewa kofar wannan gwamnati a buɗe take domin ba

da shawara musamman akan sha’anin tsaro.

 

Shina yake jawabi, mai taimakawa Gwamna Raɗɗa akan waɗanda bala’in ‘yan bindiga ya shafa. Alhaji Sa’idu Ibrahim Danja ya bayyana cewa duk jami’an tsaron ‘yan sintiri sauransu gwamnati ke ɗaukar nauyin yi masu magani idan suka sami raunuka.

 

A cewar sa yanzu haka akwai jami’an tsaro guda 4 da jama’ar gari 32 da suke kwance a asibitin koyarwa ta Katsina da kuma asibitin Ƙashi kuma gwamnatin Malam Dikko Umar Raɗɗa ke ɗaukar nauyin yi masu magani.

 

Ya ƙara da wannan naira miliyan 20 da aka ware an tsara yadda za a rabawa iyalan waɗanda wannan lamari ya shafa su talatin da uku (33) inda ya ce kowace mutum za a baiwa iyalansa naira dubu 500 da kuma iyalan wani jami’in soja da ya rasa ransa za a bashi naira miliyan ɗaya .

 

” Haka kuma muna da jami’an tsaro guda goma da suka samu raunuka wanda kuma za a baiwa kowanne su Naira dubu ɗari biyu da hamsin (250) domin su cigaba da tallafawa iyalan su” inji

 

Daga ƙarshe ya bayyana cewa waɗannan kuɗaɗen da aka ba su ba wai diyya ba ce, tallafi daga gwamna Malam Dikko Raɗɗa kuma wata hanya ce ta ƙara ƙarfafa jami’an tsaro akan wannan aiki na sadaukarwa da suke yi ba dare ba rana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansintiriKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Hana Sulhu Da ‘Yan Ta’adda Ba, Amma A Bar Jami’an Tsaro Su Yi Aikinsu – Bosso

Next Post

Harin ‘Yan Bindiga A Kauyen Dan-Umaru: ‘Yansanda Sun Kwato Roka A Kebbi

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
An Kama Masu Fataucin Kananan Yara A Ribas

Harin 'Yan Bindiga A Kauyen Dan-Umaru: 'Yansanda Sun Kwato Roka A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.